< Yohanna 12 >
1 Kwana shida kafin Bikin Ƙetarewa, sai Yesu ya iso Betani, inda Lazarus yake, wanda Yesu ya tā da daga matattu.
Seis dias antes da Páscoa, Jesus foi para Betânia, para a casa de Lázaro, a quem ele tinha ressuscitado.
2 A nan aka shirya abincin yamma don girmama Yesu. Marta ta ce yi hidima, Lazarus kuma yana ɗaya cikin waɗanda suke ci tare shi.
Ali, fizeram um jantar em sua homenagem. Marta ajudou a servir a comida, enquanto Lázaro se sentou na mesa com Jesus e com os outros convidados.
3 Sai Maryamu ta ɗauki wajen awo guda na nardi zalla, turare mai tsada; ta zuba a ƙafafun Yesu ta kuma goge ƙafafunsa da gashinta. Gidan duk ya cika da ƙanshin turaren.
Maria trouxe um frasco de perfume muito caro, feito de nardo puro, e derramou o perfume nos pés de Jesus, secando-os depois com os seus próprios cabelos. O cheiro do perfume se espalhou por toda a casa.
4 Amma ɗaya daga cikin almajiransa, Yahuda Iskariyot, wanda daga baya zai bashe shi, bai amince ba ya ce,
Mas, um dos discípulos, Judas Iscariotes, que depois iria trair Jesus, perguntou:
5 “Don me ba a sayar da turaren nan aka kuma ba da kuɗin ga matalauta ba? Ai, kuɗin ya kai albashin shekara guda.”
“Por que esse perfume não foi vendido e o dinheiro da venda dado aos pobres? Ele valeria trezentos denários.”
6 Ya yi wannan magana ba don ya kula da matalauta ba ne, sai dai don shi ɓarawo ne. Da yake shi ne mai ajiya jakar kuɗin, yakan taimaki kansa da abin da aka sa a ciki.
Ele não disse isso por estar preocupado com os pobres, mas porque era ladrão. Era ele quem cuidava do dinheiro dos discípulos e, quase sempre, pegava uma parte desse dinheiro para si.
7 Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta, an nufa ta ajiye wannan turaren don ranar jana’izata.
Jesus respondeu: “Não a critique! Ela está me preparando para o meu sepultamento.
8 Kullum za ku kasance da matalauta, amma ba kullum za ku kasance tare da ni ba.”
Os pobres sempre estarão com vocês, mas eu não estarei sempre com vocês.”
9 Ana cikin haka sai babban taron Yahudawa suka sami labari Yesu yana can suka kuwa zo, ba kawai don shi ba amma don su kuma ga Lazarus, wanda ya tā da daga matattu.
Muitas pessoas descobriram que Jesus estava lá. Elas foram até lá não apenas para ver Jesus, mas porque queriam ver Lázaro também. Afinal, ele era o homem que Jesus ressuscitara dentre os mortos.
10 Saboda haka manyan firistoci suka ƙulla su kashe Lazarus shi ma,
Então, os chefes dos sacerdotes planejaram matar Lázaro também,
11 gama dalilinsa Yahudawa da yawa suna komawa ga Yesu suna kuma ba da gaskiya gare shi.
já que ele era o motivo de tantos judeus passarem a crer em Jesus.
12 Kashegari babban taron da suka zo Bikin suka sami labari cewa Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima.
No dia seguinte, a multidão que tinha vindo para a festa da Páscoa ouviu que Jesus estava a caminho de Jerusalém.
13 Sai suka ɗaɗɗauko rassan dabino suka fiffita taryensa, suna ɗaga murya suna cewa, “Hosanna!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Mai albarka ne Sarkin Isra’ila!”
Elas cortaram folhas de palmeiras e foram dar as boas-vindas a ele, gritando: “Hosana! Que Deus abençoe aquele que vem em nome do Senhor! Que Deus abençoe o rei de Israel!”
14 Yesu ya sami ɗan jaki, ya hau, kamar yadda yake a rubuce cewa,
Jesus encontrou um jumentinho e montou nele, como as Sagradas Escrituras dizem:
15 “Kada ki ji tsoro, ya Diyar Sihiyona; duba, ga sarkinki yana zuwa, zaune a kan aholaki jaki.”
“Não tenha medo, filha de Sião! Veja! O seu rei está chegando, montado em um jumentinho!”
16 Da fari almajiransa ba su gane dukan wannan ba. Sai bayan da aka ɗaukaka Yesu, sa’an nan suka gane cewa an rubuta waɗannan abubuwa game da shi ne, har ma suka yi masa waɗannan abubuwa.
Naquela ocasião, os discípulos de Jesus não entenderam o que isso significava. Apenas tempos mais tarde, quando ele foi glorificado, eles entenderam que o que tinha acontecido havia sido escrito antes e que dizia respeito a ele.
17 Taron da suke tare da shi a sa’ad da ya kira Lazarus daga kabari ya kuma tā da shi daga matattu suka yi ta baza labarin.
Muitas pessoas na multidão tinham visto Jesus dizer a Lázaro para sair do túmulo e que ressuscitasse. E essas mesmas pessoas estavam recontando essa história.
18 Mutane da yawa kuwa suka fita taryensa, saboda sun ji labarin abin banmamakin da ya yi.
Foi por esse motivo que muitos foram ver Jesus, pois tinham ouvido falar sobre esse milagre.
19 Saboda haka Farisiyawa suka ce wa juna, “Duba, wannan ba ya kai mu ko’ina. Ga shi, duk duniya tana bin sa!”
Os fariseus disseram uns para os outros: “Veja! Nós não conseguimos resultado algum! Todos estão correndo para vê-lo!”
20 To, akwai waɗansu Hellenawa a cikin waɗanda suka haura don su yi sujada a Bikin.
Entre os que tinham ido à Jerusalém para adorar durante a festa estavam alguns gregos.
21 Suka zo wurin Filibus, wanda yake daga Betsaida ta Galili, da roƙo. Suka ce, “Ranka yă daɗe, muna so mu ga Yesu.”
Eles se aproximaram de Filipe, que era de Betsaida, na Galileia, e disseram: “Senhor, nós gostaríamos de ver Jesus!”
22 Sai Filibus ya je ya gaya wa Andarawus, Andarawus da kuma Filibus suka gaya wa Yesu.
Filipe disse isso para André. Os dois, então, foram dizer a Jesus sobre os gregos.
23 Yesu ya amsa ya ce, “Lokaci ya yi da za a ɗaukaka Ɗan Mutum.
Jesus respondeu: “Chegou o momento do Filho do Homem ser glorificado.
24 Gaskiya nake gaya muku, sai ƙwayar alkama ta fāɗi ƙasa ta mutu, in ba haka ba za tă kasance ƙwaya ɗaya tak. Amma in ta mutu, za tă ba da’ya’ya da yawa.
Eu lhes digo que isto é verdade: a menos que um grão de trigo seja plantado no solo e morra, ele ainda será apenas um grão. Mas, se ele morrer, irá produzir muitos outros grãos de trigo.
25 Duk mai ƙaunar ransa, zai rasa shi, duk mai ƙin ransa a wannan duniya, zai kiyaye shi har yă zuwa rai madawwami. (aiōnios )
Se vocês amam a sua própria vida, a perderão. Mas, se não amam a própria vida, neste mundo, vocês a manterão para a vida eterna. (aiōnios )
26 Duk wanda zai bauta mini dole yă bi ni, inda kuma nake, a can bawana zai kasance. Ubana zai girmama wanda yake bauta mini.
Se vocês quiserem me servir, precisam me seguir. Meus servos estarão onde eu estou, e o meu Pai irá honrar qualquer pessoa que me sirva.
27 “Yanzu kuwa na damu, amma me zan ce? ‘Uba, ka cece ni daga wannan sa’a’? A’a, ai, saboda wannan dalili ne musamman na zo.
Agora eu estou realmente aflito. O que eu devo dizer? Eu direi: ‘Pai, salve-me desse tempo de sofrimento que virá?’ Não, pois foi para isso que eu vim; para passar por este tempo de sofrimento.
28 Uba, ka ɗaukaka sunanka!” Sai wata murya ta fito daga sama ta ce, “Na riga na ɗaukaka shi, zan kuma ƙara ɗaukaka shi.”
Pai, mostre a glória do seu caráter.” Uma voz veio do céu e disse: “Eu já a mostrei e irei mostrá-la de novo.”
29 Taron da suke a wurin suka ji, suka ce an yi tsawa; waɗansu kuwa suka ce mala’ika ne ya yi masa magana.
A multidão que estava lá ouviu o que foi dito. Algumas pessoas disseram que tinha sido um trovão. Porém, outras disseram que um anjo tinha falado com Jesus.
30 Yesu ya ce, “An yi wannan muryar saboda amfaninku ne, ba don nawa ba.
Jesus lhes disse: “Esta voz veio não para mim, mas para vocês.
31 Yanzu ne za a yi wa duniyan nan shari’a, yanzu ne za a tumɓuke mai mulkin duniyan nan.
Agora, começa o julgamento deste mundo. Agora, o príncipe deste mundo será expulso.
32 Amma ni, sa’ad da aka ɗaga ni daga ƙasa, zan ja dukan mutane gare ni.”
Mas, quando eu for levantado da terra, atrairei todas as pessoas para mim.”
33 Ya faɗa haka ne don yă nuna irin mutuwar da zai yi.
Jesus disse isso para mostrar como iria morrer.
34 Sai taron suka ce, “Ahab, Dokarmu ta gaya mana cewa, Kiristi zai kasance har abada, to, yaya za ka ce, ‘Dole ne a ɗaga Ɗan Mutum?’ Wane ne wannan ‘Ɗan Mutum’?” (aiōn )
A multidão respondeu: “A Lei nos diz que o Messias irá viver para sempre. Então, como você pode dizer que o Filho do Homem será ‘levantado da terra’? Quem é esse ‘Filho do Homem’?” (aiōn )
35 Sai Yesu ya ce musu, “Haske zai kasance da ku na ɗan lokaci. Ku yi tafiya yayinda hasken yana nan tare da ku, kada duhu yă cim muku. Mai tafiya a cikin duhu bai san inda za shi ba.
Jesus respondeu: “A luz ficará aqui com vocês por um pouco mais de tempo. Caminhem enquanto vocês ainda têm luz, para que as trevas não os alcance. Aqueles que caminham na escuridão não sabem para onde estão indo.
36 Ku dogara ga hasken yayinda kuke da shi, don ku zama’ya’yan haske.” Da Yesu ya gama magana, sai ya tafi ya ɓuya daga gare su.
Creiam na luz enquanto vocês ainda a têm, para que, assim, possam se tornar filhos da luz.” Depois que Jesus disse isso para as pessoas, ele saiu e se ocultou delas.
37 Ko bayan Yesu ya yi dukan waɗannan abubuwan banmamaki a gabansu, duk da haka ba su gaskata da shi ba.
Mas, apesar de todos os milagres que ele fez na presença deles, eles ainda não tinham fé em Jesus.
38 Wannan ya faru ne, don a cika maganar annabi Ishaya cewa, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu, ga wa kuma aka bayyana hannun ikon Ubangiji?”
Isso aconteceu para que se cumprisse a mensagem do profeta Isaías: “Senhor, quem acreditou no que dissemos? E para quem foi revelado o poder do Senhor?”
39 Saboda haka ba su iya gaskatawa ba, domin, kamar yadda Ishaya ya faɗa a wani wuri cewa,
Eles não foram capazes de crer nele e, assim, eles cumpriram o que Isaías também tinha dito:
40 “Ya makantar da idanunsu ya kuma taurare zukatansu, don kada su gani da idanunsu, ko su fahimta a zukatansu, ko kuwa su juyo, har in warkar da su.”
“Ele cegou os olhos deles e fez com que suas mentes ficassem vazias, para que os seus olhos não pudessem ver e para que as suas mentes não pensassem e, assim, eles não se voltariam para mim, pois se eles o fizessem, eu os curaria.”
41 Ishaya ya faɗi haka ne, saboda ya hangi ɗaukakar Yesu, ya kuwa yi magana a kansa.
Isaías viu a glória de Jesus e disse isso em relação a ele.
42 Duk da haka, da yawa har daga cikin shugabanni ma suka gaskata da shi. Amma saboda Farisiyawa ba su furta bangaskiyarsu ba, don tsoron kada a kore su daga majami’a;
Até mesmo muitos dos líderes creram em Jesus. No entanto, eles não admitiram isso publicamente, porque não queriam que os fariseus os expulsassem da sinagoga.
43 gama sun fi son yabon mutane, fiye da yabon Allah.
Eles queriam mais a admiração dos homens do que a aprovação de Deus.
44 Sa’an nan Yesu ya ɗaga murya ya ce, “Duk wanda ya gaskata da ni, ba ni yake gaskatawa ba, amma ga wanda ya aiko ni ne.
Jesus disse bem alto: “Se vocês creem em mim, não estão crendo apenas em mim, mas também naquele que me enviou.
45 Duk mai dubana, yana duban wanda ya aiko ni ne.
Quando vocês me veem, também veem aquele que me enviou.
46 Na zo cikin duniya a kan ni haske ne, don duk wanda ya gaskata da ni, kada yă zauna a cikin duhu.
Eu vim como uma luz que brilha para o mundo. Então, se vocês creem em mim, não permanecerão nas trevas.
47 “Duk mai jin kalmomina bai kuwa kiyaye su ba, ba ni ba ne nake shari’anta shi. Gama ban zo domin in yi wa duniya shari’a ba, sai dai domin in cece ta.
Eu não julgo quem ouve as minhas palavras, mas não as segue. Eu vim para salvar o mundo, não para julgá-lo.
48 Akwai mai hukunci saboda wanda ya ƙi ni, bai kuma karɓi kalmomina ba; wannan maganar da na faɗa ita ce za tă hukunta shi a rana ta ƙarshe.
Qualquer pessoa que me rejeita e não aceita as minhas palavras será julgada no julgamento final de acordo com o que eu disse.
49 Gama ba don kaina na yi magana ba, Uban da ya aiko ni shi kansa ne ya ba ni umarni a kan abin da zan faɗa da kuma yadda zan faɗe shi.
Pois eu não estou falando por mim mesmo, mas pelo meu Pai, que me enviou. Foi ele quem me orientou sobre o que eu devia dizer e como dizer.
50 Na san cewa umarninsa yana kai ga rai madawwami. Saboda haka duk abin da na faɗa na faɗe shi ne kamar dai yadda Uba ya ce in faɗa.” (aiōnios )
Eu sei que o seu mandamento traz a vida eterna. Então, qualquer coisa que eu diga é o que o Pai me disse.” (aiōnios )