< Yohanna 12 >

1 Kwana shida kafin Bikin Ƙetarewa, sai Yesu ya iso Betani, inda Lazarus yake, wanda Yesu ya tā da daga matattu.
Jesus however, six days before the passover, came to Bethany, where Lazarus was, who had been dead, and whom He raised from the dead.
2 A nan aka shirya abincin yamma don girmama Yesu. Marta ta ce yi hidima, Lazarus kuma yana ɗaya cikin waɗanda suke ci tare shi.
Therefore they made Him a supper there, and Martha waited at table, but Lazarus was one of them that sat down with Him.
3 Sai Maryamu ta ɗauki wajen awo guda na nardi zalla, turare mai tsada; ta zuba a ƙafafun Yesu ta kuma goge ƙafafunsa da gashinta. Gidan duk ya cika da ƙanshin turaren.
And Mary taking a pound of ointment of spikenard of great value, anointed the feet of Jesus, and wiped them with her hair; and the house was filled with the odour of the ointment.
4 Amma ɗaya daga cikin almajiransa, Yahuda Iskariyot, wanda daga baya zai bashe shi, bai amince ba ya ce,
Therefore said one of his disciples, Judas Iscariot, the son of Simon, who was about to betray Him,
5 “Don me ba a sayar da turaren nan aka kuma ba da kuɗin ga matalauta ba? Ai, kuɗin ya kai albashin shekara guda.”
Why was not this ointment sold for three hundred pence and given to the poor?
6 Ya yi wannan magana ba don ya kula da matalauta ba ne, sai dai don shi ɓarawo ne. Da yake shi ne mai ajiya jakar kuɗin, yakan taimaki kansa da abin da aka sa a ciki.
He said this, not that he cared for the poor, but because he was a thief, and having the common purse he carried what was put into it.
7 Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta, an nufa ta ajiye wannan turaren don ranar jana’izata.
Jesus therefore said, Let her alone, she hath reserved this as for the day of my burial.
8 Kullum za ku kasance da matalauta, amma ba kullum za ku kasance tare da ni ba.”
For the poor ye have always with you, but me ye have not always.
9 Ana cikin haka sai babban taron Yahudawa suka sami labari Yesu yana can suka kuwa zo, ba kawai don shi ba amma don su kuma ga Lazarus, wanda ya tā da daga matattu.
And a great number of the Jews understanding that He was there, came not only on account of Jesus, but that they might see Lazarus also, whom He had raised from the dead.
10 Saboda haka manyan firistoci suka ƙulla su kashe Lazarus shi ma,
Wherefore the chief priests took counsel to put Lazarus also to death.
11 gama dalilinsa Yahudawa da yawa suna komawa ga Yesu suna kuma ba da gaskiya gare shi.
Because on his account many of the Jews went away from them, and believed on Jesus.
12 Kashegari babban taron da suka zo Bikin suka sami labari cewa Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima.
The next day a great multitude that were come to the feast, hearing that Jesus was coming to Jerusalem, took branches of palm-trees,
13 Sai suka ɗaɗɗauko rassan dabino suka fiffita taryensa, suna ɗaga murya suna cewa, “Hosanna!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Mai albarka ne Sarkin Isra’ila!”
and went out to meet Him, and cried, Hosanna! blessed be the king of Israel, who cometh in the name of the Lord.
14 Yesu ya sami ɗan jaki, ya hau, kamar yadda yake a rubuce cewa,
And Jesus having gotten a young ass sat thereon,
15 “Kada ki ji tsoro, ya Diyar Sihiyona; duba, ga sarkinki yana zuwa, zaune a kan aholaki jaki.”
as it is written, "Fear not, O daughter of Sion, behold thy king cometh sitting on an ass's colt."
16 Da fari almajiransa ba su gane dukan wannan ba. Sai bayan da aka ɗaukaka Yesu, sa’an nan suka gane cewa an rubuta waɗannan abubuwa game da shi ne, har ma suka yi masa waɗannan abubuwa.
Now his disciples did not understand these things at the first: but when Jesus was glorified, then they remembered that these things were written concerning Him, and that they had done thus unto Him.
17 Taron da suke tare da shi a sa’ad da ya kira Lazarus daga kabari ya kuma tā da shi daga matattu suka yi ta baza labarin.
And the people that were with Him testified, that He called Lazarus out of the grave, and raised him from the dead:
18 Mutane da yawa kuwa suka fita taryensa, saboda sun ji labarin abin banmamakin da ya yi.
and for this reason the people went to meet Him, because they heard that He had done this miracle.
19 Saboda haka Farisiyawa suka ce wa juna, “Duba, wannan ba ya kai mu ko’ina. Ga shi, duk duniya tana bin sa!”
The pharisees therefore said among themselves, Do ye not see that ye prevail nothing? Behold, all the world is gone after Him.
20 To, akwai waɗansu Hellenawa a cikin waɗanda suka haura don su yi sujada a Bikin.
And among those that came up to worship at the feast there were certain Greeks:
21 Suka zo wurin Filibus, wanda yake daga Betsaida ta Galili, da roƙo. Suka ce, “Ranka yă daɗe, muna so mu ga Yesu.”
that came to Philip who was of Bethsaida in Galilee, and asked him, saying, Sir, we have a desire to see Jesus.
22 Sai Filibus ya je ya gaya wa Andarawus, Andarawus da kuma Filibus suka gaya wa Yesu.
And Philip cometh and telleth Andrew, and then Andrew and Philip told Jesus.
23 Yesu ya amsa ya ce, “Lokaci ya yi da za a ɗaukaka Ɗan Mutum.
And Jesus answered them saying, The time is come that the Son of man is to be glorified.
24 Gaskiya nake gaya muku, sai ƙwayar alkama ta fāɗi ƙasa ta mutu, in ba haka ba za tă kasance ƙwaya ɗaya tak. Amma in ta mutu, za tă ba da’ya’ya da yawa.
Though I tell you indeed and in truth, Except a grain of wheat fall into the ground and die, it remaineth alone; but if it die, it produceth much fruit.
25 Duk mai ƙaunar ransa, zai rasa shi, duk mai ƙin ransa a wannan duniya, zai kiyaye shi har yă zuwa rai madawwami. (aiōnios g166)
So he, that loveth his life, shall lose it; and he that hateth his life in this world, shall preserve it unto life eternal. (aiōnios g166)
26 Duk wanda zai bauta mini dole yă bi ni, inda kuma nake, a can bawana zai kasance. Ubana zai girmama wanda yake bauta mini.
If any man would serve me, let him follow me; and where I am, there shall also my servant be: and if any one serve me, him will my Father honour.
27 “Yanzu kuwa na damu, amma me zan ce? ‘Uba, ka cece ni daga wannan sa’a’? A’a, ai, saboda wannan dalili ne musamman na zo.
Now is my soul troubled, and what shall I say? Father, save me from this hour: but for this cause came I to this hour.
28 Uba, ka ɗaukaka sunanka!” Sai wata murya ta fito daga sama ta ce, “Na riga na ɗaukaka shi, zan kuma ƙara ɗaukaka shi.”
Father, glorify thy name. Then came a voice from heaven, saying, I have both glorified it, and will glorify it again.
29 Taron da suke a wurin suka ji, suka ce an yi tsawa; waɗansu kuwa suka ce mala’ika ne ya yi masa magana.
The people therefore that stood by, and heard it, said, That it was thunder: but others said, it was an angel spake to Him.
30 Yesu ya ce, “An yi wannan muryar saboda amfaninku ne, ba don nawa ba.
Jesus answered and said, This voice came not for my sake, but for yours.
31 Yanzu ne za a yi wa duniyan nan shari’a, yanzu ne za a tumɓuke mai mulkin duniyan nan.
Now is the judgement of this world: now shall the prince of this world be cast out.
32 Amma ni, sa’ad da aka ɗaga ni daga ƙasa, zan ja dukan mutane gare ni.”
And I, when I am lifted up from the earth, shall draw all men unto me.
33 Ya faɗa haka ne don yă nuna irin mutuwar da zai yi.
This He said, signifying what death He should die.
34 Sai taron suka ce, “Ahab, Dokarmu ta gaya mana cewa, Kiristi zai kasance har abada, to, yaya za ka ce, ‘Dole ne a ɗaga Ɗan Mutum?’ Wane ne wannan ‘Ɗan Mutum’?” (aiōn g165)
The people answered Him, We have heard out of the law, that the Messiah abideth for ever: and how sayest thou, the Son of man must be lifted up? who is this Son of man? (aiōn g165)
35 Sai Yesu ya ce musu, “Haske zai kasance da ku na ɗan lokaci. Ku yi tafiya yayinda hasken yana nan tare da ku, kada duhu yă cim muku. Mai tafiya a cikin duhu bai san inda za shi ba.
Then Jesus said unto them, Yet a little while the light is to be with you; walk while ye have the light, least darkness overtake you; for he that walketh in the dark knoweth not whither he goeth.
36 Ku dogara ga hasken yayinda kuke da shi, don ku zama’ya’yan haske.” Da Yesu ya gama magana, sai ya tafi ya ɓuya daga gare su.
While ye have the light, believe in the light, that ye may be the children of light. These things spake Jesus, and then went away, and concealed himself from them.
37 Ko bayan Yesu ya yi dukan waɗannan abubuwan banmamaki a gabansu, duk da haka ba su gaskata da shi ba.
But though He had done so many miracles before their eyes, yet they did not believe on Him:
38 Wannan ya faru ne, don a cika maganar annabi Ishaya cewa, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu, ga wa kuma aka bayyana hannun ikon Ubangiji?”
so that the word of Esaias the prophet was fulfilled, which he spake, saying, Lord, who hath believed our report? and to whom hath the arm of the Lord been revealed?
39 Saboda haka ba su iya gaskatawa ba, domin, kamar yadda Ishaya ya faɗa a wani wuri cewa,
And therefore they could not believe; for Esaias had also said,
40 “Ya makantar da idanunsu ya kuma taurare zukatansu, don kada su gani da idanunsu, ko su fahimta a zukatansu, ko kuwa su juyo, har in warkar da su.”
He hath blinded their eyes, and hardened their heart, that they might not see with their eyes, and understand with their heart, and be converted, and I should heal them.
41 Ishaya ya faɗi haka ne, saboda ya hangi ɗaukakar Yesu, ya kuwa yi magana a kansa.
These things said Esaias when he saw his glory, and spake concerning Him.
42 Duk da haka, da yawa har daga cikin shugabanni ma suka gaskata da shi. Amma saboda Farisiyawa ba su furta bangaskiyarsu ba, don tsoron kada a kore su daga majami’a;
There were however many of the chief rulers that believed on Him; but because of the pharisees they did not confess it, lest they should be excommunicated.
43 gama sun fi son yabon mutane, fiye da yabon Allah.
For they loved the praise of men more than the praise of God.
44 Sa’an nan Yesu ya ɗaga murya ya ce, “Duk wanda ya gaskata da ni, ba ni yake gaskatawa ba, amma ga wanda ya aiko ni ne.
And Jesus raised his voice, and said, He that believeth on me, believeth not on me only, but on Him that sent me:
45 Duk mai dubana, yana duban wanda ya aiko ni ne.
and he that beholdeth me, beholdeth Him that sent me.
46 Na zo cikin duniya a kan ni haske ne, don duk wanda ya gaskata da ni, kada yă zauna a cikin duhu.
I am come a light into the world, that whosoever believeth on me, might not abide in darkness.
47 “Duk mai jin kalmomina bai kuwa kiyaye su ba, ba ni ba ne nake shari’anta shi. Gama ban zo domin in yi wa duniya shari’a ba, sai dai domin in cece ta.
And if any one hear my words and believe not, I do not condemn him: for I am not now come to condemn the world, but to save the world.
48 Akwai mai hukunci saboda wanda ya ƙi ni, bai kuma karɓi kalmomina ba; wannan maganar da na faɗa ita ce za tă hukunta shi a rana ta ƙarshe.
He that rejecteth me, and receiveth not my words, hath one that judgeth him: the word, that I have spoken, will condemn him at the last day.
49 Gama ba don kaina na yi magana ba, Uban da ya aiko ni shi kansa ne ya ba ni umarni a kan abin da zan faɗa da kuma yadda zan faɗe shi.
For I have not spoken of myself; but the Father, who sent me, gave me a commandment, what I should say and what I should speak.
50 Na san cewa umarninsa yana kai ga rai madawwami. Saboda haka duk abin da na faɗa na faɗe shi ne kamar dai yadda Uba ya ce in faɗa.” (aiōnios g166)
And I know that his commandment is life eternal: the things therefore which I speak, I so speak, as the Father hath directed me. (aiōnios g166)

< Yohanna 12 >