< Yohanna 12 >

1 Kwana shida kafin Bikin Ƙetarewa, sai Yesu ya iso Betani, inda Lazarus yake, wanda Yesu ya tā da daga matattu.
Jesus, however, six days before the Passover, came to Bethany, where Lazarus was whom He had raised from the dead.
2 A nan aka shirya abincin yamma don girmama Yesu. Marta ta ce yi hidima, Lazarus kuma yana ɗaya cikin waɗanda suke ci tare shi.
So they gave a dinner there in honour of Jesus, at which Martha waited at table, but Lazarus was one of the guests who were with Him.
3 Sai Maryamu ta ɗauki wajen awo guda na nardi zalla, turare mai tsada; ta zuba a ƙafafun Yesu ta kuma goge ƙafafunsa da gashinta. Gidan duk ya cika da ƙanshin turaren.
Availing herself of the opportunity, Mary took a pound weight of pure spikenard, very costly, and poured it over His feet, and wiped His feet with her hair, so that the house was filled with the fragrance of the perfume.
4 Amma ɗaya daga cikin almajiransa, Yahuda Iskariyot, wanda daga baya zai bashe shi, bai amince ba ya ce,
Then said Judas (the Iscariot, one of the Twelve--the one who afterwards betrayed Jesus),
5 “Don me ba a sayar da turaren nan aka kuma ba da kuɗin ga matalauta ba? Ai, kuɗin ya kai albashin shekara guda.”
"Why was not that perfume sold for 300 shillings and the money given to the poor?"
6 Ya yi wannan magana ba don ya kula da matalauta ba ne, sai dai don shi ɓarawo ne. Da yake shi ne mai ajiya jakar kuɗin, yakan taimaki kansa da abin da aka sa a ciki.
The reason he said this was not that he cared for the poor, but that he was a thief, and that being in charge of the money-box, he used to steal what was put into it.
7 Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta, an nufa ta ajiye wannan turaren don ranar jana’izata.
But Jesus interposed. "Do not blame her," He said, "allow her to have kept it for the time of my preparation for burial.
8 Kullum za ku kasance da matalauta, amma ba kullum za ku kasance tare da ni ba.”
For the poor you always have with you, but you have not me always."
9 Ana cikin haka sai babban taron Yahudawa suka sami labari Yesu yana can suka kuwa zo, ba kawai don shi ba amma don su kuma ga Lazarus, wanda ya tā da daga matattu.
Now it became widely known among the Jews that Jesus was there; but they came not only on His account, but also in order to see Lazarus whom He had brought back to life.
10 Saboda haka manyan firistoci suka ƙulla su kashe Lazarus shi ma,
The High Priests, however, consulted together to put Lazarus also to death,
11 gama dalilinsa Yahudawa da yawa suna komawa ga Yesu suna kuma ba da gaskiya gare shi.
for because of him many of the Jews left them and became believers in Jesus.
12 Kashegari babban taron da suka zo Bikin suka sami labari cewa Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima.
The next day a great crowd of those who had come to the Festival, hearing that Jesus was coming to Jerusalem,
13 Sai suka ɗaɗɗauko rassan dabino suka fiffita taryensa, suna ɗaga murya suna cewa, “Hosanna!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Mai albarka ne Sarkin Isra’ila!”
took branches of the palm trees and went out to meet Him, shouting as they went, "God save him! Blessings on him who comes in the name of the Lord--even on the King of Israel!"
14 Yesu ya sami ɗan jaki, ya hau, kamar yadda yake a rubuce cewa,
And Jesus, having procured a young ass, sat upon it, just as the Scripture says,
15 “Kada ki ji tsoro, ya Diyar Sihiyona; duba, ga sarkinki yana zuwa, zaune a kan aholaki jaki.”
"Fear not, Daughter of Zion! See, thy King is coming riding on an ass's colt."
16 Da fari almajiransa ba su gane dukan wannan ba. Sai bayan da aka ɗaukaka Yesu, sa’an nan suka gane cewa an rubuta waɗannan abubuwa game da shi ne, har ma suka yi masa waɗannan abubuwa.
The meaning of this His disciples did not understand at the time; but after Jesus was glorified they recollected that this was written about Him, and that they had done this to Him.
17 Taron da suke tare da shi a sa’ad da ya kira Lazarus daga kabari ya kuma tā da shi daga matattu suka yi ta baza labarin.
The large number of people, however, who had been present when He called Lazarus out of the tomb and brought him back to life, related what they had witnessed.
18 Mutane da yawa kuwa suka fita taryensa, saboda sun ji labarin abin banmamakin da ya yi.
This was also why the crowd came to meet Him, because they had heard of His having performed that miracle.
19 Saboda haka Farisiyawa suka ce wa juna, “Duba, wannan ba ya kai mu ko’ina. Ga shi, duk duniya tana bin sa!”
The result was that the Pharisees said among themselves, "Observe how idle all your efforts are! The world is gone after him!"
20 To, akwai waɗansu Hellenawa a cikin waɗanda suka haura don su yi sujada a Bikin.
Now some of those who used to come up to worship at the Festival were Greeks.
21 Suka zo wurin Filibus, wanda yake daga Betsaida ta Galili, da roƙo. Suka ce, “Ranka yă daɗe, muna so mu ga Yesu.”
They came to Philip, of Bethsaida in Galilee, with the request, "Sir, we wish to see Jesus."
22 Sai Filibus ya je ya gaya wa Andarawus, Andarawus da kuma Filibus suka gaya wa Yesu.
Philip came and told Andrew: Andrew and Philip told Jesus.
23 Yesu ya amsa ya ce, “Lokaci ya yi da za a ɗaukaka Ɗan Mutum.
His answer was, "The time has come for the Son of Man to be glorified.
24 Gaskiya nake gaya muku, sai ƙwayar alkama ta fāɗi ƙasa ta mutu, in ba haka ba za tă kasance ƙwaya ɗaya tak. Amma in ta mutu, za tă ba da’ya’ya da yawa.
In most solemn truth I tell you that unless the grain of wheat falls into the ground and dies, it remains what it was--a single grain; but that if it dies, it yields a rich harvest.
25 Duk mai ƙaunar ransa, zai rasa shi, duk mai ƙin ransa a wannan duniya, zai kiyaye shi har yă zuwa rai madawwami. (aiōnios g166)
He who holds his life dear, is destroying it; and he who makes his life of no account in this world shall keep it to the Life of the Ages. (aiōnios g166)
26 Duk wanda zai bauta mini dole yă bi ni, inda kuma nake, a can bawana zai kasance. Ubana zai girmama wanda yake bauta mini.
If a man wishes to be my servant, let him follow me; and where I am, there too shall my servant be. If a man wishes to be my servant, the Father will honour him.
27 “Yanzu kuwa na damu, amma me zan ce? ‘Uba, ka cece ni daga wannan sa’a’? A’a, ai, saboda wannan dalili ne musamman na zo.
Now is my soul full of trouble; and what shall I say? Father, save me from this hour. But for this purpose I have come to this hour.
28 Uba, ka ɗaukaka sunanka!” Sai wata murya ta fito daga sama ta ce, “Na riga na ɗaukaka shi, zan kuma ƙara ɗaukaka shi.”
Father, glorify Thy name." Thereupon there came a voice from the sky, "I have glorified it and will also glorify it again."
29 Taron da suke a wurin suka ji, suka ce an yi tsawa; waɗansu kuwa suka ce mala’ika ne ya yi masa magana.
The crowd that stood by and heard it, said that there had been thunder. Others said, "An angel spoke to him."
30 Yesu ya ce, “An yi wannan muryar saboda amfaninku ne, ba don nawa ba.
"It is not for my sake," said Jesus, "that that voice came, but for your sakes.
31 Yanzu ne za a yi wa duniyan nan shari’a, yanzu ne za a tumɓuke mai mulkin duniyan nan.
Now is a judgement of this world: now will the Prince of this world be driven out.
32 Amma ni, sa’ad da aka ɗaga ni daga ƙasa, zan ja dukan mutane gare ni.”
And I-- if I am lifted up from the earth--will draw all men to me."
33 Ya faɗa haka ne don yă nuna irin mutuwar da zai yi.
He said this to indicate the kind of death He would die.
34 Sai taron suka ce, “Ahab, Dokarmu ta gaya mana cewa, Kiristi zai kasance har abada, to, yaya za ka ce, ‘Dole ne a ɗaga Ɗan Mutum?’ Wane ne wannan ‘Ɗan Mutum’?” (aiōn g165)
The crowd answered Him, "We have heard out of the Law that the Christ remains for ever. In what sense do you say that the Son of Man must be lifted up? Who is that Son of Man?" (aiōn g165)
35 Sai Yesu ya ce musu, “Haske zai kasance da ku na ɗan lokaci. Ku yi tafiya yayinda hasken yana nan tare da ku, kada duhu yă cim muku. Mai tafiya a cikin duhu bai san inda za shi ba.
"Yet a little while," He replied, "the light is among you. Be faithful to the light that you have, for fear darkness should overtake you; for a man who walks in the dark does not know where he is going.
36 Ku dogara ga hasken yayinda kuke da shi, don ku zama’ya’yan haske.” Da Yesu ya gama magana, sai ya tafi ya ɓuya daga gare su.
In the degree that you have light, believe in the Light, so that you may become sons of Light." Jesus said this, and went away and hid Himself from them.
37 Ko bayan Yesu ya yi dukan waɗannan abubuwan banmamaki a gabansu, duk da haka ba su gaskata da shi ba.
But though He had performed such great miracles in their presence, they did not believe in Him--
38 Wannan ya faru ne, don a cika maganar annabi Ishaya cewa, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu, ga wa kuma aka bayyana hannun ikon Ubangiji?”
in order that the words of Isaiah the Prophet might be fulfilled, "Lord, who has believed our preaching? And the arm of the Lord--to whom has it been unveiled?"
39 Saboda haka ba su iya gaskatawa ba, domin, kamar yadda Ishaya ya faɗa a wani wuri cewa,
For this reason they were unable to believe--because Isaiah said again,
40 “Ya makantar da idanunsu ya kuma taurare zukatansu, don kada su gani da idanunsu, ko su fahimta a zukatansu, ko kuwa su juyo, har in warkar da su.”
"He has blinded their eyes and made their minds callous, lest they should see with their eyes and perceive with their minds, and should turn, and I should heal them."
41 Ishaya ya faɗi haka ne, saboda ya hangi ɗaukakar Yesu, ya kuwa yi magana a kansa.
Isaiah uttered these words because he saw His glory; and he spoke of Him.
42 Duk da haka, da yawa har daga cikin shugabanni ma suka gaskata da shi. Amma saboda Farisiyawa ba su furta bangaskiyarsu ba, don tsoron kada a kore su daga majami’a;
Nevertheless even from among the Rulers many believed in Him. But because of the Pharisees they did not avow their belief, for fear they should be shut out from the synagogue.
43 gama sun fi son yabon mutane, fiye da yabon Allah.
For they loved the glory that comes from men rather than the glory that comes from God.
44 Sa’an nan Yesu ya ɗaga murya ya ce, “Duk wanda ya gaskata da ni, ba ni yake gaskatawa ba, amma ga wanda ya aiko ni ne.
But Jesus cried aloud, "He who believes in me, believes not so much in me, as in Him who sent me;
45 Duk mai dubana, yana duban wanda ya aiko ni ne.
and he who sees me sees Him who sent me.
46 Na zo cikin duniya a kan ni haske ne, don duk wanda ya gaskata da ni, kada yă zauna a cikin duhu.
I have come like light into the world, in order that no one who believes in me may remain in the dark.
47 “Duk mai jin kalmomina bai kuwa kiyaye su ba, ba ni ba ne nake shari’anta shi. Gama ban zo domin in yi wa duniya shari’a ba, sai dai domin in cece ta.
And if any one hears my teachings and regards them not, I do not judge him; for I did not come to judge the world, but to save the world.
48 Akwai mai hukunci saboda wanda ya ƙi ni, bai kuma karɓi kalmomina ba; wannan maganar da na faɗa ita ce za tă hukunta shi a rana ta ƙarshe.
He who sets me at naught and does not receive my teachings is not left without a judge: the Message which I have spoken will judge him on the last day.
49 Gama ba don kaina na yi magana ba, Uban da ya aiko ni shi kansa ne ya ba ni umarni a kan abin da zan faɗa da kuma yadda zan faɗe shi.
Because I have not spoken on my own authority; but the Father who sent me, Himself gave me a command what to say and in what words to speak.
50 Na san cewa umarninsa yana kai ga rai madawwami. Saboda haka duk abin da na faɗa na faɗe shi ne kamar dai yadda Uba ya ce in faɗa.” (aiōnios g166)
And I know that His command is the Life of the Ages. What therefore I speak, I speak just as the Father has bidden me." (aiōnios g166)

< Yohanna 12 >