< Yohanna 11 >
1 To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
Kwakulendoda eyayithiwa nguLazaro eyayigula. YayingeyaseBhethani, umuzi okwakuhlala khona uMariya lodadewabo uMatha.
2 Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
(UMariya lo olomnewabo uLazaro owayephethwe ngumkhuhlane nguye owathela amakha ezinyaweni zeNkosi wazesula ngenwele zakhe.)
3 Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
Ngakho odadewabo laba bathumela ilizwi kuJesu bathi, “Nkosi, lowo omthandayo uyagula.”
4 Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
UJesu esekuzwile lokhu wathi, “Ukugula lokhu kakuzukucina ngokufa. Kodwa kungokodumo lukaNkulunkulu ukuze iNdodana kaNkulunkulu idunyiswe ngakho.”
5 Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
UJesu wayemthanda uMatha lodadewabo kanye loLazaro.
6 Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
Kodwa loba esezwile ukuthi uLazaro wayegula wazihlalela khona lapho ayekhona okwezinye insuku ezimbili.
7 Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
Wasesithi kubafundi bakhe, “Kasibuyeleni eJudiya.”
8 Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
Bathi, “Oh, Rabi, muvana nje amaJuda ake azama ukukukhanda ngamatshe kodwa wena usubuyela khona futhi?”
9 Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
UJesu waphendula wathi, “Kakusikho yini ukuthi kulamahola alitshumi lambili okukhanyisa kwelanga na? Umuntu ohamba emini kayikukhubeka ngoba ebona ngokukhanya kwalapha emhlabeni.
10 Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
Ukhubeka nxa ehamba ebusuku ngoba kalakho ukukhanya.”
11 Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
Esekutshilo lokhu wasebatshela wathi, “Umngane wethu uLazaro uselele kodwa ngiya khonale ukuyamvusa.”
12 Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
Abafundi bakhe baphendula bathi, “Nkosi, nxa kuvuma ukuthi alale, uzabangcono.”
13 Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
UJesu wayekhuluma ngokufa kwakhe kodwa abafundi bakhe babesithi kumbe utsho ukulala okujayelekileyo.
14 Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
Wasebatshela ephumela egcekeni wathi, “ULazaro usefile,
15 amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
kodwa ukuze lina likholwe, ngiyathaba ukuthi bengingekho lapho. Kodwa kasiyeni khona.”
16 Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
UThomasi (othiwa nguDidimasi) wathi kwabanye abafundi, “Lathi kasihambeni ukuze siyekufa laye.”
17 Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
Ekufikeni kwakhe uJesu uLazaro wayesehlale ethuneni okwensuku ezine.
18 Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
EBhethani kwakungaphansi kwamakhilomitha amathathu usuka eJerusalema,
19 Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
yikho amaJuda amanengi ayebuyile ukuzakhalela uMatha loMariya ngokulahlekelwa kwabo ngumnewabo.
20 Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
Kwathi uMatha esizwa ukuthi uJesu wayesiza, waphuma wamhlangabeza kodwa uMariya wasala ngekhaya.
21 Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
UMatha wathi kuJesu, “Nkosi, aluba ubukhonapha ngabe umnewethu kafanga.
22 Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
Kodwa ngiyazi ukuthi lamanje uNkulunkulu uzakunika loba yini oyicelayo.”
23 Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
UJesu wathi kuye, “Umfowenu uzavuka njalo.”
24 Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
UMatha waphendula wathi, “Ngiyazi ukuthi uzavuka futhi ekuvukeni kwabafileyo ngosuku lokucina.”
25 Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
UJesu wathi kuye, “Mina ngiyikuvuka kwabafileyo lokuphila. Lowo okholwa kimi uzaphila loba engafa;
26 kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn )
njalo lowo ophilayo ekholwa kimi kasoze afa lanini. Uyakukholwa lokhu na?” (aiōn )
27 Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
Waphendula wathi, “Yebo Nkosi, ngiyakholwa ukuthi unguye uKhristu, iNdodana kaNkulunkulu, ozabuya emhlabeni.”
28 Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
Esekutshilo lokho wabuyela ngekhaya wabizela udadewabo uMariya eceleni wathi, “UMfundisi usekhona, uyakucela.”
29 Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
UMariya wathi ekuzwa lokhu wasuka masinyane waya kuJesu.
30 Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
UJesu wayelokhu engakangeni phakathi komuzi elokhu elapho ayehlangane khona loMatha.
31 Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
Kwathi amaJuda ayeloMariya endlini emduduza esebonile ukuthi wasukuma masinyane njani ephuma, amlandela ecabanga ukuthi mhlawumbe wayesiya ethuneni ukuyakhalela khona.
32 Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
UMariya wonela ukufika lapho uJesu ayekhona, wambona, wazilahla phansi ezinyaweni zakhe wathi, “Nkosi, kube ubukhona lapha, umnewethu ngabe kafanga.”
33 Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
UJesu embona ekhala kanye lamaJuda ayemlandele wadabuka kakhulu emoyeni, wakhathazeka.
34 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
Wabuza wathi, “Limbeke ngaphi na?” Baphendula bathi, “Woza uzobona Nkosi.”
36 Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
AmaJuda asesithi, “Liyabona ukuthi wayemthanda njani!”
37 Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
Kodwa amanye awo athi, “Kanti yena lo owavula amehlo endoda eyayiyisiphofu wehlulekile ukwenza ukuthi umuntu lo angafi na?”
38 Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
UJesu waphinda njalo wadabuka, wasondela ethuneni. Ithuna lalilubhalu, kulelitshe elalivale intuba.
39 Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
Wathi, “Lisuseni ilitshe.” UMatha, udadewabo wendoda efileyo wathi, “Nkosi, khathesi sekulephunga elibi ngoba selensuku ezine simbekile.”
40 Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
UJesu wasesithi, “Kangikutshelanga ukuthi nxa ukholwa uzabona inkazimulo kaNkulunkulu na?”
41 Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
Ngakho balisusa ilitshe. UJesu wasekhangela phezulu wathi, “Baba ngiyakubonga ukuthi ungizwile.
42 Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
Mina bengisazi ukuthi uhlala ungizwa, kodwa ngikutshela lokhu ngisenzela abantu abemi lapha ukuze bakholwe ukuthi ungithumile.”
43 Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
Esekutshilo lokhu uJesu wamemeza ngelizwi elikhulu wathi, “Lazaro, phuma!”
44 Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
Umuyi waphuma, izandla lenyawo zakhe zithandelwe ngamaqhele elineni, kulelinye ilembu elalembese ubuso bakhe. UJesu wathi kubo, “Khuphani izivunulo zokungcwaba limyekele ahambe.”
45 Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
Ngakho amaJuda amanengi ayeze ukuzakhalela uMariya esekubonile uJesu akwenzayo, amkholwa.
46 Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
Kodwa amanye aya kubaFarisi bayabatshela lokho okwakwenziwe nguJesu.
47 Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
Abaphristi abakhulu labaFarisi basebebiza umhlangano weSanihedrini. Babuzana bathi, “Kanti sivele senzani? Nangu phela umuntu lo esenza imimangaliso eminengi.
48 In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
Singamyekela aqhubeke ngalindlela, wonke umuntu uzakholwa kuye njalo amaRoma azakuza athathe indawo yethu lesizwe sethu.”
49 Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
Kwasekusithi omunye wabo owayethiwa nguKhayifasi, owayengumphristi omkhulu ngalowomnyaka, wakhuluma wathi, “Kalazi lutho!
50 Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
Kalikuboni lina ukuthi kungcono ukuba umuntu oyedwa afele abantu kulokuthi kubhubhe isizwe sonke.”
51 Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
Lokhu kazikhulumelanga yena ngokwakhe, kodwa njengomphristi omkhulu kwabanye ngalowomnyaka waphrofitha ukuthi uJesu wayezafela isizwe samaJuda,
52 ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
kungasisizwe leso sodwa, kodwa labantwana bakaNkulunkulu abahlakazekileyo ukuze balethwe ndawonye, benziwe babemunye.
53 Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
Kusukela ngalesosikhathi bakha amacebo okumbulala.
54 Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
Ngakho uJesu wayengasahambahambi obala phakathi kwamaJuda. Wasuka lapho waya emangweni owawuseduze kwenkangala, emzini owawuthiwa yi-Efrayimu, lapho ahlala khona labafundi bakhe.
55 Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
Kwathi sekuzakuba yisikhathi sePhasika lamaJuda, abanengi baqubuka elizweni baya eJerusalema ukuyahlanjululwa ngokomkhuba kungakabi yiPhasika.
56 Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
Babelokhu bethalaza befuna uJesu, kwathi bemi egumeni lethempeli babuzana bathi, “Licabangani? Ukuthi angaphutha yini emkhosini?”
57 Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.
Kodwa abaphristi abakhulu labaFarisi basebelayele ukuthi nxa ekhona owayekwazi ukuthi uJesu wayengaphi, ahle abike ukuze bambophe.