< Yohanna 11 >

1 To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
איש בשם אלעזר, שגר בבית־עניה עם מרים ואחותה מרתא, חלה. אחותו מרים היא זו שמשחה את ישוע במרקחת יקרה וניגבה את רגליו בשערותיה.
2 Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
3 Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
מרתא ומרים שלחו הודעה לישוע:”אדוני, ידידך הטוב חולה מאוד.“
4 Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
כששמע ישוע את הדבר אמר:”מחלה זאת לא תיגמר במוות, כי אם להביא כבוד לאלוהים. כי בן האלוהים יפואר באמצעות המחלה הזאת.“
5 Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
ישוע אהב מאוד את מרתא, מרים ואלעזר.
6 Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
כאשר ישוע שמע שאלעזר חלה, התעכב יומיים
7 Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
ורק לאחר מכן אמר לתלמידיו:”הבה נחזור ליהודה.“
8 Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
”אולם, רבי, “קראו התלמידים במחאה,”לפני ימים ספורים בלבד ניסו מנהיגי היהודים להרוג אותך, ועכשיו אתה חוזר לאותו מקום?“
9 Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
”בכל יום יש שתים־עשרה שעות אור, ובמשך השעות האלה יכול כל אחד ללכת בלי ליפול או להיכשל.
10 Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
מי שהולך בלילה ייכשל וימעד בגלל החשכה.“
11 Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
ישוע המשיך:”חברנו אלעזר ישן, אך אני הולך להעיר אותו.“
12 Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
ישוע התכוון לכך שאלעזר מת, אולם תלמידיו חשבו שאמר כי אלעזר ישן במנוחה, ולכן אמרו:”אם אלעזר ישן שינה טובה הוא ודאי יבריא!“
13 Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
14 Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
”אלעזר מת“, אמר להם ישוע בפירוש.
15 amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
”אני שמח למענכם שלא הייתי שם, כדי שתלמדו להאמין. הבה נלך אליו.“
16 Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
תומא (הנקרא בשם חיבה”התאום“) אמר לחבריו התלמידים:”בואו נלך גם אנחנו כדי שנמות איתו.“
17 Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
בהגיעם לבית־עניה נאמר להם שאלעזר מת ושהוא קבור כבר ארבעה ימים.
18 Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
בית־עניה מרוחקת מירושלים רק כשלושה קילומטר,
19 Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
ויהודים רבים באו מירושלים לנחם את מרתא ומרים באבלן.
20 Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
כאשר שמעה מרתא שישוע היה בדרכו אליהן, הלכה לפגוש אותו, ואילו מרים נשארה בבית.
21 Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
”אדוני, “אמרה מרתא לישוע,”אילו היית כאן, אחי לא היה מת.
22 Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
אך עדיין לא מאוחר מדי, כי אני יודעת שכל מה שתבקש מאלוהים הוא ייתן לך.“
23 Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
”אחיך יקום לחיים“, הבטיח ישוע.
24 Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
”כן, “אמרה מרתא,”עם כל האחרים בתחיית המתים ביום האחרון.“
25 Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
אולם ישוע אמר לה:”אני הוא התחייה והחיים. כל המאמין בי יחיה אפילו אם ימות.
26 kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn g165)
כל המאמין בי יחיה לנצח ולא ימות לעולם! האם את מאמינה לי?“ (aiōn g165)
27 Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
”כן, אדוני, “השיבה,”אני מאמינה שאתה המשיח בן־האלוהים אשר לו חיכינו זמן רב.“
28 Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
כשסיימה מרתא לדבר עזבה את ישוע וחזרה למרים. מרתא קראה למרים בסתר ואמרה:”המורה נמצא כאן; הוא רוצה לדבר איתך.“
29 Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
מרים יצאה אליו מיד.
30 Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
ישוע נשאר עדיין מחוץ לכפר, במקום שבו פגשה אותו מרתא.
31 Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
היהודים שבאו לנחם את האבלות ראו את מרים עוזבת את הבית בחיפזון. הם חשבו שהיא הולכת לבכות על קבר אחיה, ולכן הלכו בעקבותיה.
32 Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
כאשר הגיעה מרים למקום הימצאו של ישוע, נפלה לרגליו וקראה בבכי:”אדוני, אילו היית כאן, אחי לא היה מת.“
33 Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
בכייה ובכי האבלים נגע ללבו של ישוע, וגם הוא התרגש ונאנח.
34 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
”היכן קברתם אותו?“שאל.”בוא וראה“, ענו האנשים.
35 Yesu ya yi kuka.
ישוע בכה.
36 Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
”הם היו חברים טובים מאוד“, אמרו היהודים זה לזה.”ראו עד כמה אהב אותו!“
37 Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
היו שאמרו:”אם הוא ריפא את העיוור, האם לא היה יכול גם למנוע את מותו של אלעזר?“
38 Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
ישוע שוב התרגש והלך אל קברו של אלעזר. הוא נקבר במערה שאבן גדולה חסמה את פיתחה.
39 Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
”הזיזו את האבן“, ביקש ישוע. אולם מרתא, אחות המת, אמרה:”אבל אדוני, הגופה ודאי מצחינה; הרי הוא קבור כבר ארבעה ימים!“
40 Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
”האם לא אמרתי לך שאם תאמיני תראי את גבורת האלוהים?“שאל ישוע.
41 Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
האנשים הזיזו את האבן, וישוע נשא עיניו אל השמים וקרא:”אבי, תודה לך על שאתה שומע אותי.
42 Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
אני יודע שאתה שומע אותי תמיד, אולם אמרתי זאת כדי שכל הנוכחים כאן יאמינו שאתה שלחת אותי.“
43 Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
לאחר מכן הוא קרא בקול רם מאוד:”אלעזר, צא החוצה!“
44 Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
ואלעזר יצא החוצה עטוף עדיין בתכריכים.”הסירו מעליו את התכריכים ותנו לו ללכת“, אמר ישוע.
45 Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
יהודים רבים מבין מנחמי מרים אשר חזו בנס האמינו בישוע.
46 Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
אולם היו שהלכו לפרושים וסיפרו להם את הדבר.
47 Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
הפרושים וראשי הכוהנים כינסו אסיפה כדי לדון במצב.”איפה הוא ואיפה אנחנו?“שאלו זה את זה במבוכה.”האיש הזה באמת מחולל ניסים!
48 In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
אם לא נאסור אותו יאמין בו כל העם וילך אחריו, וזה יהיה סופנו, כי אז יבואו הרומאים ויסירו את בית המקדש ואת עמנו!“
49 Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
קייפא, הכהן הגדול באותה שנה, אמר להם:”אינכם מבינים דבר!
50 Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
האינכם מבינים כי מוטב שאדם אחד ימות בעד כל העם, מאשר שכל העם ימות בעד אדם אחד? למה לסכן את העם?“
51 Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
קייפא לא אמר דברים אלה ביוזמתו, אלא בהשראת אלוהים, כי בהיותו הכהן הגדול של אותה שנה ניבא שישוע ימות בעד העם.
52 ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
ולא רק בעד העם, אלא גם כדי לקבץ ולאחד את כל בני־האלוהים באשר הם.
53 Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
מאותו יום ואילך תכננו מנהיגי היהודים להרוג את ישוע,
54 Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
ולכן הוא הפסיק להתהלך בגלוי באזור יהודה. הוא עזב את ירושלים והחליט ללכת לעיר אפרים שבגבול המדבר, שם נשאר עם תלמידיו.
55 Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
בהתקרב חג הפסח עלו לירושלים יהודים רבים מכל קצות הארץ, כדי להשתתף בטקס הטהרה שקדם לחג.
56 Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
הם רצו לראות את ישוע, ובעמדם בבית־המקדש שאלו איש את רעהו:”מה דעתכם, האם יבוא לחג הפסח או לא?“
57 Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.
בינתיים הודיעו ראשי הכוהנים והפרושים בציבור, שכל הרואה את ישוע חייב לדווח להם על כך מיד, כדי שיוכלו לאסרו.

< Yohanna 11 >