< Yohanna 11 >
1 To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
And there was a certain one ailing, Lazarus, from Bethany, of the village of Mary and Martha her sister —
2 Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
and it was Mary who did anoint the Lord with ointment, and did wipe his feet with her hair, whose brother Lazarus was ailing —
3 Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
therefore sent the sisters unto him, saying, 'Sir, lo, he whom thou dost love is ailing;'
4 Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
and Jesus having heard, said, 'This ailment is not unto death, but for the glory of God, that the Son of God may be glorified through it.'
5 Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
And Jesus was loving Martha, and her sister, and Lazarus,
6 Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
when, therefore, he heard that he is ailing, then indeed he remained in the place in which he was two days,
7 Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
then after this, he saith to the disciples, 'We may go to Judea again;'
8 Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
the disciples say to him, 'Rabbi, now were the Jews seeking to stone thee, and again thou dost go thither!'
9 Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
Jesus answered, 'Are there not twelve hours in the day? if any one may walk in the day, he doth not stumble, because the light of this world he doth see;
10 Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
and if any one may walk in the night, he stumbleth, because the light is not in him.'
11 Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
These things he said, and after this he saith to them, 'Lazarus our friend hath fallen asleep, but I go on that I may awake him;'
12 Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
therefore said his disciples, 'Sir, if he hath fallen asleep, he will be saved;'
13 Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
but Jesus had spoken about his death, but they thought that about the repose of sleep he speaketh.
14 Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
Then, therefore, Jesus said to them freely, 'Lazarus hath died;
15 amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
and I rejoice, for your sake, (that ye may believe, ) that I was not there; but we may go to him;'
16 Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
therefore said Thomas, who is called Didymus, to the fellow-disciples, 'We may go — we also, that we may die with him,'
17 Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
Jesus, therefore, having come, found him having been four days already in the tomb.
18 Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
And Bethany was nigh to Jerusalem, about fifteen furlongs off,
19 Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
and many of the Jews had come unto Martha and Mary, that they might comfort them concerning their brother;
20 Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
Martha, therefore, when she heard that Jesus doth come, met him, and Mary kept sitting in the house.
21 Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
Martha, therefore, said unto Jesus, 'Sir, if thou hadst been here, my brother had not died;
22 Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
but even now, I have known that whatever thou mayest ask of God, God will give to thee;'
23 Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
Jesus saith to her, 'Thy brother shall rise again.'
24 Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
Martha saith to him, 'I have known that he will rise again, in the rising again in the last day;'
25 Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
Jesus said to her, 'I am the rising again, and the life; he who is believing in me, even if he may die, shall live;
26 kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn )
and every one who is living and believing in me shall not die — to the age; (aiōn )
27 Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
believest thou this?' she saith to him, 'Yes, sir, I have believed that thou art the Christ, the Son of God, who is coming to the world.'
28 Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
And these things having said, she went away, and called Mary her sister privately, saying, 'The Teacher is present, and doth call thee;'
29 Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
she, when she heard, riseth up quickly, and doth come to him;
30 Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
and Jesus had not yet come to the village, but was in the place where Martha met him;
31 Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
the Jews, therefore, who were with her in the house, and were comforting her, having seen Mary that she rose up quickly and went forth, followed her, saying — 'She doth go away to the tomb, that she may weep there.'
32 Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
Mary, therefore, when she came where Jesus was, having seen him, fell at his feet, saying to him, 'Sir, if thou hadst been here, my brother had not died;'
33 Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
Jesus, therefore, when he saw her weeping, and the Jews who came with her weeping, did groan in the spirit, and troubled himself, and he said,
34 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
'Where have ye laid him?' they say to him, 'Sir, come and see;'
36 Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
The Jews, therefore, said, 'Lo, how he was loving him!'
37 Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
and certain of them said, 'Was not this one, who did open the eyes of the blind man, able to cause that also this one might not have died?'
38 Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
Jesus, therefore, again groaning in himself, cometh to the tomb, and it was a cave, and a stone was lying upon it,
39 Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
Jesus saith, 'Take ye away the stone;' the sister of him who hath died — Martha — saith to him, 'Sir, already he stinketh, for he is four days dead;'
40 Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
Jesus saith to her, 'Said I not to thee, that if thou mayest believe, thou shalt see the glory of God?'
41 Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
They took away, therefore, the stone where the dead was laid, and Jesus lifted his eyes upwards, and said, 'Father, I thank Thee, that Thou didst hear me;
42 Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
and I knew that Thou always dost hear me, but, because of the multitude that is standing by, I said [it], that they may believe that Thou didst send me.'
43 Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
And these things saying, with a loud voice he cried out, 'Lazarus, come forth;'
44 Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
and he who died came forth, being bound feet and hands with grave-clothes, and his visage with a napkin was bound about; Jesus saith to them, 'Loose him, and suffer to go.'
45 Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
Many, therefore, of the Jews who came unto Mary, and beheld what Jesus did, believed in him;
46 Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
but certain of them went away unto the Pharisees, and told them what Jesus did;
47 Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
the chief priests, therefore, and the Pharisees, gathered together a sanhedrim, and said, 'What may we do? because this man doth many signs?
48 In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
if we may let him alone thus, all will believe in him; and the Romans will come, and will take away both our place and nation.'
49 Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
and a certain one of them, Caiaphas, being chief priest of that year, said to them, 'Ye have not known anything,
50 Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
nor reason that it is good for us that one man may die for the people, and not the whole nation perish.'
51 Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
And this he said not of himself, but being chief priest of that year, he did prophesy that Jesus was about to die for the nation,
52 ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
and not for the nation only, but that also the children of God, who have been scattered abroad, he may gather together into one.
53 Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
From that day, therefore, they took counsel together that they may kill him;
54 Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
Jesus, therefore, was no more freely walking among the Jews, but went away thence to the region nigh the wilderness, to a city called Ephraim, and there he tarried with his disciples.
55 Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
And the passover of the Jews was nigh, and many went up to Jerusalem out of the country before the passover, that they might purify themselves;
56 Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
they were seeking, therefore, Jesus, and said one with another, standing in the temple, 'What doth appear to you — that he may not come to the feast?'
57 Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.
and both the chief priests and the Pharisees had given a command, that if any one may know where he is, he may shew [it], so that they may seize him.