< Yohanna 11 >

1 To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
A certayne man was sicke named Lazarus of Bethania the toune of Mary and her sister Martha.
2 Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
It was that Mary which annoynted Iesus with oyntment and wyped his fete with her heere whose brother Lazarus was sicke
3 Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
and his sisters sent vnto him sayinge. Lorde behold he whom thou lovest is sicke.
4 Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
When Iesus hearde yt he sayd: this infirmite is not vnto deth but for ye laude of God that the sonne of God myght be praysed by the reason of it.
5 Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
Iesus loved Martha and her sister and Lazarus.
6 Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
After he hearde that he was sicke then aboode he two dayes still in the same place where he was.
7 Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
Then after that sayd he to his disciples: let us goo into Iewry agayne.
8 Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
His disciples sayde vnto him. Master the Iewes lately sought meanes to stone the and wilt thou goo thyther agayne?
9 Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
Iesus answered: are ther not twelve houres in ye daye? Yf a man walke in ye daye he stombleth not because he seith the lyght of this worlde.
10 Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
But yf a ma walke in ye nyght he stombleth because ther is no lyght in him.
11 Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
This sayde he and after yt he sayde vnto the: oure frende Lazarus slepeth but I goo to wake him out of slepe.
12 Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
Then sayde his disciples: Lorde yf he slepe he shall do well ynough.
13 Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
How be it Iesus spake of his deeth: but they thought yt he had spoke of ye naturall slepe.
14 Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
Then sayde Iesus vnto the playnly Lazarus is deed
15 amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
and I am glad for youre sakes yt I was not there because ye maye beleve. Neverthelesse let vs go vnto him.
16 Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
Then sayde Thomas which is called Dydimus vnto ye disciples: let vs also goo that we maye dye wt him
17 Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
Then went Iesus and founde that he had lyne in his grave foure dayes already.
18 Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
Bethanie was nye vnto Ierusalem aboute. xv. furlonges of
19 Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
and many of the Iewes were come to Martha and Mary to comforte them over their brother.
20 Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
Martha assone as she hearde yt Iesus was comynge went and met him: but Mary sate still in the housse.
21 Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
Then sayde Martha vnto Iesus: Lorde yf thou haddest bene here my brother had not bene deed:
22 Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
but neverthelesse I knowe that whatsoever thou axest of God God will geve it the.
23 Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
Iesus sayde vnto her: Thy brother shall ryse agayne.
24 Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
Martha sayde vnto him: I knowe that he shall ryse agayne in the resurreccion at the last daye.
25 Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
Iesus sayde vnto her: I am the resurreccion and the lyfe: He that beleveth on me ye though he were deed yet shall he lyve.
26 kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn g165)
And whosoever lyveth and belevest on me shall never dye. Beleveth thou this? (aiōn g165)
27 Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
She sayde vnto him: ye Lorde I beleve that thou arte Christ the sonne of god which shuld come into the worlde.
28 Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
And assone as she had so sayde she went her waye and called Marie her sister secretly sayinge: The master is come and calleth for the
29 Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
And she assone as she hearde that arose quickly and came vnto him.
30 Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
Iesus was not yet come into the toune: but was in the place where Martha met him.
31 Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
The Iewes then which were with her in the housse and comforted her when they sawe Mary that she rose vp hastely and went out folowed her saying: She goeth vnto the grave to wepe there.
32 Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
Then when Mary was come where Iesus was and sawe him she fell doune at his fete sayinge vnto him: Lorde yf thou haddest bene here my brother had not bene deed.
33 Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
When Iesus sawe her wepe and ye Iewes also wepe which came wt her he groned in ye sprete and was troubled in him selfe
34 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
and sayde: Where have ye layed him? They sayde vnto him: Lorde come and se.
35 Yesu ya yi kuka.
And Iesus wept.
36 Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
Then sayde the Iewes: Beholde howe he loved him.
37 Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
And some of the sayde: coulde not he which openned the eyes of the blynde have made also that this man shuld not have dyed?
38 Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
Iesus agayne groned in him selfe and came to the grave. It was a caue and a stone layde on it.
39 Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
And Iesus sayd: take ye awaye the stone. Martha the sister of him that was deed sayd vnto him: Lorde by this tyme he stinketh. For he hath bene deed foure dayes:
40 Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
Iesus sayde vnto her: Sayde I not vnto the yt if thou didest beleve thou shuldest se ye glory of God.
41 Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
Then they toke awaye ye stone from ye place where the deed was layde. And Iesus lyfte vp his eyes and sayde: Father I thanke the because that thou hast hearde me.
42 Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
I wot that thou hearest me all wayes: but because of the people that stonde by I sayde it yt they maye beleve that thou hast sent me.
43 Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
And when he thus had spoken he cryed wt a loud voyce. Lazarus come forthe.
44 Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
And he that was deed came forth bounde hand and fote with grave bondes and his face was bounde with a napkin. Iesus sayde vnto the: loowse him and let him goo.
45 Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
Then many of the Iewes which came to Mary and had sene the thinges which Iesus dyd beleved on him.
46 Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
But some of them went their wayes to the Pharises and tolde them what Iesus had done.
47 Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
Then gadered the hye prestes and the Pharises a counsell and sayde: what do we? This ma doeth many miracles.
48 In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
Yf we let him scape thus all men will beleve on him and ye Romaynes shall come and take awaye oure countre and the people.
49 Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
And one of them named Cayphas which was the hieprest yt same yeare sayde vnto them: Ye perceave nothinge at all
50 Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
nor yet consider that it is expedient for vs that one man dye for the people and not that all the people perisshe.
51 Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
This spake he not of him selfe but beinge hye preste that same yeare he prophesied that Iesus shulde dye for the people
52 ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
and not for the people only but that he shuld gader to geder in one the chyldren of God which were scattered abroode.
53 Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
From that daye forth they held a counsell to geder for to put him to deeth.
54 Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
Iesus therfore walked no more opely amoge the Iewes: but wet his waye thence vnto a coutre nye to a wildernes into a cite called Ephraim and there hauted with his disciples.
55 Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
And the Iewes ester was nye at hand and many went out of the countre vp to Ierusalem before the ester to purify them selves.
56 Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
Then sought they for Iesus and spake bitwene the selves as they stode in the teple: What thinke ye seynge he cometh not to the feast.
57 Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.
The hye prestes and Pharises had geven a comaundemet that yf eny man knew where he were he shuld shewe it that they myght take him.

< Yohanna 11 >