< Yohanna 11 >

1 To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
BUT a certain man was sick, Loozar, of the village Bethania: (he was) the brother of Mariam and of Martha.
2 Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
It was that Mariam who anointed with balsam the feet of Jeshu, and wiped (them) with her hair, whose brother this Loozar was who was sick.
3 Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
And his two sisters sent unto Jeshu, saying, Our Lord, he whom thou lovest is sick.
4 Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
But Jeshu said, This sickness is not of death, but for the glory of Aloha, that the Son of Aloha may be glorified on account of it.
5 Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
But Jeshu loved Martha and Mariam and Loozar.
6 Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
And when he heard that he was sick, he remained in the place where he was two days.
7 Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
And afterwards he saith to his disciples, Come, we will go again into Jihud.
8 Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
His disciples say to him, Raban, now have the Jihudoyee sought to stone thee; and again goest thou thither?
9 Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
Jeshu saith to them, Are there not twelve hours in the day? If a man walk in the day, he stumbleth not, because he seeth the light of this world;
10 Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
but if a man walk in the night, he stumbleth, because no light is in him.
11 Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
These spake Jeshu; and afterwards he said to them, Loozar our friend reposeth; but I go to awake him.
12 Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
His disciples say to him, Our Lord, if he sleep he is healed.
13 Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
But Jeshu spake concerning his death; and they thought that concerning the repose of sleep he spake.
14 Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
Then said Jeshu to them explicatively, Loozar is dead.
15 amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
And I am glad I was not there for your sakes, that you may believe. But let us walk thither.
16 Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
Thoma, who is called the Twin, saith to his fellow-disciples, Let us also go, that we may die with him.
17 Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
And Jeshu came to Bethania, and found that he had been four days in the house of burial.
18 Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
Now Bethania was nigh to Urishlem, being a distance from it of about fifteen stadia.
19 Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
And many of the Jihudoyee had come to Martha and Mariam, that they might speak to their hearts concerning their brother.
20 Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
Then Martha, when she heard that Jeshu had come, went forth to meet him; but Mariam sat in the house.
21 Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
And Martha said to Jeshu, My Lord, if thou hadst been here, my brother had not died.
22 Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
But even now know I that whatsoever thou wilt ask of Aloha, he giveth to thee.
23 Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
Jeshu saith to her, Thy brother ariseth.
24 Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
Martha saith to him, I know that he ariseth in the resurrection at the last day.
25 Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
Jeshu saith to her, I am the Resurrection and the Life; and (he) who believeth in me, although he will die, shall live.
26 kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn g165)
And every one who liveth and believeth in me, for ever shall not die. Believest thou this? (aiōn g165)
27 Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
She saith to him, Yes, my Lord; I believe that thou art the Meshicha, the Son of Aloha, who cometh into the world.
28 Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
And when she had said these, she went, called Mariam her sister in secret, and said to her, Our Master hath come, and calleth for thee.
29 Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
When Mariam heard, she arose quickly, and came to him.
30 Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
But Jeshu himself had not yet come into the village, but was in that place where Martha met him.
31 Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
But those Jihudoyee who were also with her in the house to console her, when they saw that Mariam rose up hastily to go forth, went themselves after her; for they thought that to the sepulchre she went to weep.
32 Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
But she, Mariam, when she was come where Jeshu was, and saw him, fell down at his feet, saying, If thou hadst been here, my Lord, my brother had not died.
33 Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
But Jeshu, when he saw her weeping, and those Jihudoyee who came with her weeping, he was moved in his spirit, and was troubled,
34 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
and said, Where have you laid him? And they said to him, Our Lord, come and see.
35 Yesu ya yi kuka.
And the tears of Jeshu came.
36 Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
And the Jihudoyee said, See how he loved him!
37 Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
But some of them said, Could not this who opened the eyes of that blind have caused also that this should not have died?
38 Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
Jeshu, groaning within himself, came to the house of burial; and that house of burial was a cave, and a stone was laid at the gate of it.
39 Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
And Jeshu said, Take up this stone. Martha, the sister of him (who was) dead, saith to him, My Lord, he now stinketh; for four days are to him.
40 Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
Jeshu said to her, Said I not to thee, that if thou wilt believe, thou shalt see the glory of Aloha?
41 Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
And they took up the stone. And Jeshu lifted his eye upward, and said, Father, I give thanks to thee that thou hast heard me;
42 Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
and I know that at all times thou hearest me: yet, because of this assembly which standeth, I say these (words), that they may believe that thou hast sent me.
43 Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
And when he had said these (words), he cried with a high voice, Loozar, come without!
44 Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
And he, the dead, came forth, his hands and his feet being bound with bandages, and his face in a linen cloth. Jeshu saith to them, Release him, and let (him) go.
45 Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
And many of the Jihudoyee who came with Mariam, when they saw the thing which Jeshu did, believed on him.
46 Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
And some of them went to the Pharishee, and told them every thing that Jeshu had done.
47 Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
AND the chief priests and Pharishee assembled, and said, What shall we do? because this man doeth many signs;
48 In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
and if we leave him thus, all men will believe on him, and the Rumoyee, coming, take away our country and our people.
49 Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
But one of them, whose name was Kaiapha, was the high priest of that year; and he said to them, You know not any thing,
50 Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
nor reason that it is expedient for us that one man die for the people, and not all the people perish.
51 Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
But this from himself he spake not, but because he was high priest of that year, he prophesied that Jeshu should die for the people,
52 ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
and not only for (that) people, but also that the children of Aloha who are dispersed he should gather into one.
53 Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
And from that day they determined to kill him.
54 Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
But Jeshu himself walked not openly among the Jihudoyee, but went from thence to the region near the wilderness, to a region which was called Ephrem, and there conversed with his disciples.
55 Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
NOW the petscha of the Jihudoyee drew nigh; and many went up from the country places to Urishlem before the festival, to purify themselves.
56 Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
And they sought for Jeshu, and said one to another in the temple, What think you, that he cometh to the feast?
57 Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.
But the chief priests and Pharishee had commanded that if any man knew where (he was), he should declare it to them, as that they might apprehend him.

< Yohanna 11 >