< Yohanna 11 >

1 To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
Now a certain man was sick, Lazarus of Bethany, of the village of Mary and Martha her sister.
2 Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
And Mary was she who anointed the Lord with perfume, and wiped his feet with her hair—whose brother Lazarus was sick.
3 Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
The sisters, therefore, sent out unto him, saying—Lord, see! he whom thou tenderly lovest, is sick.
4 Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
But Jesus hearing, said—This sickness, is not unto death, but for the glory of God, —that the Son of God may be glorified thereby.
5 Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
Now Jesus loved Martha, and her sister, and Lazarus.
6 Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
When, therefore, he heard that he was sick, then, indeed, he abode in the place where he was, two days.
7 Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
Then, after this, he saith unto the disciples—Let us be leading on into Judaea, again.
8 Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
The disciples say unto him—Rabbi! just now, were the Jews seeking to stone thee—and, again, goest thou thither?
9 Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
Jesus answered—Are there not, twelve hours, in the day? If one walk in the day, he doth no stumble, because, the light of this world, he seeth;
10 Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
But, if one walk in the night, he stumbleth, because, the light, is not in him.
11 Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
These things, he said, and, after this, he saith unto them—Lazarus, our dear friend, hath fallen asleep; but I am going, that I may awake him.
12 Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
The disciples, therefore, said unto him—Lord! if he have fallen asleep, he will recover.
13 Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
But Jesus had spoken concerning his death; whereas, they, supposed that, concerning the taking of rest in sleep, he had been speaking.
14 Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
Jesus, therefore, then, said unto them, plainly, —Lazarus, died;
15 amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
and I rejoice, for your sake—that ye may believe, —that I was not there; but let us be going unto him.
16 Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
Thomas, therefore, the one called Didymus, said unto his fellow-disciples—Let, us also, be going, that we may die with him.
17 Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
Jesus, therefore, coming, found that, four days already, had he been in the tomb.
18 Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
Now Bethany was near Jerusalem, about fifteen furlongs off;
19 Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
and, many from among the Jews, had come unto Martha and Mary, that they might console them concerning their brother.
20 Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
Martha, therefore, when she heard that Jesus was coming, went to meet him; but, Mary, in the house, remained sitting.
21 Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
Martha, therefore, said unto Jesus—Lord! if thou hadst been here, my brother had not died;
22 Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
And, now, I know, that, whatsoever thou shalt ask of God, God, will give unto thee.
23 Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
Jesus saith unto her—Thy brother shall rise.
24 Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
Martha saith unto him, I know that he shall rise, in the resurrection, in the last day.
25 Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
Jesus said unto her—I, am the resurrection, and the life: he that believeth on me, even though he die, shall live again!
26 kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn g165)
And, no one who liveth again and believeth on me, shall in anywise die, unto times age-abiding. Believest thou this? (aiōn g165)
27 Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
She saith unto him—Yea, Lord! I, have believed, that, thou, art the Christ, the Son of God, —He who, into the world, should come.
28 Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
And this saying, she went away, and called Mary her sister, secretly, saying—The teacher, is present, and calleth thee.
29 Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
And, she, when she heard, was roused up quickly, and was coming unto him.
30 Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
Not yet, however, had Jesus come into the village, but was still in the place where, Martha, met him.
31 Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
The Jews, therefore, who were with her in the house and consoling her, seeing Mary, that quickly she arose and went out, followed her, supposing that she was withdrawing unto the tomb, that she might weep there.
32 Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
Mary, therefore, when she came where Jesus was, seeing him, fell at his feet, saying unto him—Lord! if thou hadst been here, my brother had not died.
33 Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
Jesus, therefore, when he saw her weeping, and the Jews who came with her weeping, was indignant in the spirit, and troubled himself,
34 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
and said—Where have ye laid him? They say unto him—Lord! come and see.
35 Yesu ya yi kuka.
Jesus wept.
36 Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
The Jews, therefore, were saying—See! how tenderly he loved him!
37 Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
But, some from among them, said—Could not this man, who opened the eyes of the blind, have caused that, this one also, should not have died?
38 Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
Jesus, therefore, again, being indignant within himself, cometh unto the tomb. Now it was a cave, and, a stone, was lying thereon.
39 Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
Jesus, saith, Take ye away the stone! Martha, the sister of the deceased, saith unto him—Lord! by this time, he stinketh, for it is, four days.
40 Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
Jesus saith unto her—Said I not unto thee, that, if thou wouldst believe, thou shouldst see the glory of God?
41 Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
So they took away the stone. And, Jesus, lifted up his eyes on high, and said—Father! I thank thee, thou didst hear me:
42 Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
I, indeed, knew that, always, unto me, thou dost hearken; but, for the sake of the multitude standing around, I spake, —that they might believe that, thou, didst send me forth.
43 Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
And, these things, having said, with a loud voice, he cried out—Lazarus! Come forth!
44 Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
He that was dead came forth, bound feet and hands with bandages, and, his face, with a napkin, was bound about. Jesus saith unto them—Loose him, and let him go.
45 Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
Many therefore from among the Jews, who had come unto Mary, and gazed on what he did, believed on him
46 Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
but, certain from among them, went away unto the Pharisees, and told them what Jesus had done.
47 Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
The High-priests and Pharisees, therefore, brought together a high-council, and were saying—What are we to do, in that, this man, doeth, many signs?
48 In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
If we let him alone thus, all, will believe on him, and the Romans will come, and take away, both our place and nation.
49 Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
But, a certain one from among them, Caiaphas, being, High-priest, for that year, said unto them—Ye, know, nothing at all;
50 Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
nor do ye take into account, that it is profitable for you that, one man, should die for the people, and not, the whole nation, perish.
51 Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
This, however, from himself, he spake not, but, being, High-priest, for that year, he prophesied, that Jesus was about to die for the nation;
52 ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
and, not for the nation only, but that, the scattered children of God also, he might gather together into one.
53 Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
From that day, therefore, they took counsel, that they might put him to death.
54 Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
Jesus, therefore, no longer openly, was walking among the Jews, but departed thence, into the country near the desert, unto a city called, Ephraim; and, there, abode, with his disciples.
55 Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
Now the passover of the Jews was at hand, and many went up unto Jerusalem, out of the country, before the passover, that they might purify themselves.
56 Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
They were therefore seeking Jesus, and were saying one to another, in the temple, standing—How seemeth it unto you? that he will in nowise come unto the feast?
57 Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.
Now the High-priests and the Pharisees had given commands, that, if anyone came to know where he was, he should inform [them], so that they might seize him.

< Yohanna 11 >