< Yohanna 11 >

1 To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
在伯大尼有一位名叫拉撒路的病人,与他的姐妹玛利亚和马大住在一起。
2 Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
这就是那位后来在主头上抹香膏、用头发擦干主双脚的玛利亚,患病的拉撒路是她的兄弟。
3 Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
姐妹二人让其他人向耶稣捎去一个口信:“主啊,你的好朋友病了。”
4 Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
耶稣听见这个消息就说:“这病不至于死,通过他的病将显示上帝的荣光,让上帝之子获得荣耀。”
5 Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
尽管耶稣喜爱马大、玛利亚和拉撒路,
6 Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
但听说拉撒路病了,他没有马上过去,而是继续在当地住了两天。
7 Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
然后他对门徒说:“我们回到犹太去吧。”
8 Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
门徒对他说:“拉比,几天前犹太人还想用石头打你,你真的想要现在就回去吗?”
9 Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
耶稣回答:“白昼不是有十二小时吗?在白昼行走不会跌倒,因为这世界上有光。
10 Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
若在夜间行走就会跌倒,因为你没有光。”
11 Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
耶稣说完这番话,继续说:“我们的朋友拉撒路睡着了,但我要去那里唤醒他!”
12 Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
门徒们说:“主啊,既然他睡了,就会好过来的。”
13 Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
其实耶稣在暗指拉撒路已死,门徒却以为他真的睡着了。
14 Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
于是,耶稣明确地告诉他们:“拉撒路死了。
15 amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
因为你们的原因,我很高兴我当时不在那里,因为现在你们就可以相信我了。现在我们去看看他吧。”
16 Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
孪生兄弟之一多马对其他门徒说:“我们也一起去吧,我们可以与他一同赴死。”
17 Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
耶稣到了伯大尼,得知拉撒路四天前被安葬在坟墓里。
18 Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
伯大尼与耶路撒冷相距约有三公里。
19 Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
有许多犹太人来到马大和玛利亚那里,为拉撒路的死表示哀悼。
20 Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
马大听见耶稣来了,就去迎接他,玛利亚却仍然呆在家里。
21 Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
马大对耶稣说:“主啊,如果你早在这里,我的兄弟就不会死了。
22 Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
就是现在,我确定无论你向上帝求什么,上帝必赐给你。”
23 Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
耶稣对她说:“你的兄弟将会复活。”
24 Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
马大回答:“我知道在末日重生之际,他必会再次站立起来。”
25 Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
耶稣说:“我就是复活,我就是生命,信我之人可死而再次站立起来。
26 kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn g165)
所有活着又相信我之人,必定永远不死,你信这话吗?” (aiōn g165)
27 Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
她说:“是的,主啊,我相信你就是基督,是上帝之子,是众人期盼降临这世界之人。”
28 Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
马大说罢,就回去叫她的姐妹玛利亚,偷偷地说:“老师来了,他要见你。”
29 Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
玛利亚听言急忙站起来去见耶稣。
30 Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
当时耶稣还没有进入村子,仍然站在马大与他相见的地点。
31 Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
有些犹太人在房子里安慰玛利亚,见她匆忙起身出门,于是就跟着她,以为她要到坟墓那边痛哭。
32 Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
玛利亚来到耶稣面前,见到就立刻伏倒在他脚前说:“主啊,如果你当时在这里,我的兄弟就不会死了!”
33 Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
见到她和跟来的犹太人在面前哭泣,耶稣心中万分悲伤难过。。
34 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
他问到:“你们把他安葬在哪里?” 他们回答说:“主啊,快来看吧。”
35 Yesu ya yi kuka.
耶稣也流下了眼泪。
36 Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
犹太人说:“你看,他多么爱这个人。”
37 Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
但也有人说:“他既然能让盲人重见光明,难道不能让拉撒路不要死去吗?”
38 Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
耶稣分外难过地来到坟墓前面,这是一个洞穴,洞口堵着一块石头。
39 Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
耶稣吩咐众人:“把这块石头挪开。” 但死者的姐妹马大说:“主啊,他已经死去四天了,味道一定特别难闻。”
40 Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
耶稣说:“还记得我对你说过的吗?如果你相信我,就会看到上帝的荣耀。”
41 Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
于是他们挪开石头。耶稣举目望天,说:“父啊,感谢你聆听我,
42 Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
我知道你总是在聆听我,但我说这番话是为了站在这里的民众,为了让他们相信,是你派我而来。”
43 Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
说罢,耶稣大喊:“拉撒路,出来吧!”
44 Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
那死去的人便走出来,手脚都缠着布,脸上也裹着布。 耶稣说:“解开布吧,放他自由!”
45 Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
到玛利亚那里奔丧的犹太人看到耶稣的所为,于是信了他。
46 Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
但他们中间有些人还是去了法利赛人那里,讲述了耶稣的所作所为。
47 Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
于是牧师长和法利赛人召开公议会,说:“这个人显化了许多神迹,我们该怎么办?
48 In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
如果我们任由他继续,所有人都会信他,罗马人就会过来摧毁我们的圣殿,消灭我们的民族。”
49 Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
该亚法是当年的大牧师,他说:“你们什么都不知道,
50 Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
难道看不出来吗?让一个人代替民众而死,免得整个民族灭亡,这样做对你们更好。”
51 Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
他这样说并非为了自己着想,而是因为他是那年的大牧师,所以预言耶稣要替这个民族死。
52 ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
这样做不只是为了犹太民族,还是为了散落各地的上帝之子,将他们聚在一起成为一体。
53 Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
从那天起,他们就开始密谋如何杀害耶稣。
54 Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
所以耶稣不再在犹太人中间公开活动,而是去了荒漠附近一个名叫以法莲的城市,与门徒一起住在那里。
55 Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
犹太人的逾越节快到了,许多人在节前从四乡八里来到耶路撒冷洁净自己。
56 Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
他们到处寻找耶稣,站在圣殿里彼此说:“你们觉得呢?他会来过节吗?”
57 Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.
牧师长和法利赛人早已下了命令:任何人知道耶稣在哪里,都应来此举报,他们将逮捕他。

< Yohanna 11 >