< Yohanna 10 >

1 “Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma.
DE cierto, de cierto os digo [que] el que no entra por la puerta en el corral de las ovejas, mas sube por otra parte, el tal es ladron y robador.
2 Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne.
Mas el que entra por la puerta, el pastor de las ovejas es.
3 Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje.
A este abre el portero, y las ovejas oyen su voz; y á sus ovejas llama por nombre y las saca.
4 Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa.
Y como ha sacado fuera todas las propias, va delante de ellas: y las ovejas le siguen, porque conocen su voz.
5 Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.”
Mas al extraño no seguirán, ántes huirán de él; porque no conocen la voz de los extraños.
6 Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.
Esta parábola les dijo Jesus; mas ellos no entendieron qué era lo que les decia.
7 Saboda haka Yesu ya sāke cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ni ne ƙofar tumakin.
Volvióles pues Jesus á decir: De cierto, de cierto os digo, que yo soy la puerta de las ovejas.
8 Duk waɗanda suka riga ni zuwa ɓarayi ne,’yan fashi kuma, amma tumakin ba su saurare su ba.
Todos los que ántes de mí vinieron, ladrones son y robadores; mas no los oyeron las ovejas.
9 Ni ne ƙofar; duk wanda ya shiga ta wurina zai sami ceto. Zai riƙa shiga yă fita yă kuwa sami wurin kiwo.
Yo soy la puerta: el que por mí entrare, será salvo; y entrará, y saldrá, y hallará pastos.
10 Ɓarawo yakan zo don yă yi sata ne kawai da kisa da kuma ɓarna. Ni kuwa na zo ne don su sami rai, su kuma same shi a yalwace.
El ladron no viene sino para hurtar, y matar, y destruir [las ovejas: ] yo he venido para que tengan vida, y para que [la] tengan en abundancia.
11 “Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yakan ba da ransa domin tumakin.
Yo soy el buen pastor: el buen pastor su vida da por [sus] ovejas.
12 Wanda aka ɗauko haya ba shi ne makiyayi mai tumakin ba. Saboda haka sa’ad da ya ga kyarkeci yana zuwa, sai yă sheƙa da gudu yă bar tumakin. Sai kyarkecin yă kai wa garken hari, yă kuma watsar da su.
Mas el asalariado, y que no es el pastor, de quien no son propias las ovejas, ve al lobo que viene, y deja las ovejas, y huye; y el lobo las arrebata, y esparce las ovejas.
13 Mutumin yakan gudu don shi ɗan haya ne kawai, bai kuwa damu da tumakin ba.
Así que el asalariado huye, porque es asalariado, y no tiene cuidado de las ovejas.
14 “Ni ne makiyayi mai kyau; na san tumakina, tumakina kuma sun san ni,
Yo soy el buen pastor; y conozco mis [ovejas, ] las mias me conocen.
15 kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uba, ina kuwa ba da raina domin tumakin.
Como el Padre me conoce [á mí, ] y yo conozco al Padre: y pongo mi vida por las ovejas.
16 Ina da waɗansu tumaki da ba na wannan garken ba ne. Dole ne in kawo su su ma. Za su saurari muryata, za su kasance garke guda ɗaya, makiyayi guda kuma.
Tambien tengo otras ovejas que no son de este redil: aquellas tambien me conviene traer, y oirán mi voz; y habrá un rebaño, y un pastor.
17 Abin da ya sa Ubana yake ƙaunata ke nan, domin ina ba da raina, in ɗauko shi kuma.
Por eso me ama el Padre, porque yo pongo mi vida, para volverla á tomar.
18 Ba mai karɓe mini rai, ina dai ba da shi. Ina da iko in ba da shi, ina da iko in ɗauko shi kuma. Wannan umarni kuwa daga wurin Ubana na karɓo shi.”
Nadie me la quita, mas yo la pongo de mí mismo; [porque] tengo poder para ponerla, y tengo poder para volverla á tomar. Este mandamiento recibí de mi Padre.
19 Saboda waɗannan kalmomi fa, sai ɓaraka ta sāke shiga cikin Yahudawa.
Y volvió á haber disension entre los Judíos por estas palabras.
20 Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”
Y muchos de ellos decian: Demonio tiene, y está fuera de sí: ¿^para qué le oís?
21 Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
Decian otros: Estas palabras no son de endemoniado: ¿puede el demonio abrir los ojos de los ciegos?
22 Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
Y se hacia la fiesta de la dedicacion en Jerusalem, y era invierno.
23 Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
Y Jesus andaba en el templo por el portal de Salomon.
24 sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
Y rodeáronle los Judíos, y dijéronle: ¿Hasta cuándo nos has de turbar el alma? Si tú eres el Cristo, dínos[lo] abiertamente.
25 Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
Respondióles Jesus: Os [lo] he dicho, y no creeis: las obras que yo hago en nombre de mi Padre, ellas dan testimonio de mí.
26 Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
Mas vosotros no creeis, porque no sois de mis ovejas, como os he dicho.
27 Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
Mis ovejas oyen mi voz, y yo las conozco, y me siguen;
28 Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn g165, aiōnios g166)
Y yo les doy vida eterna; y no perecerán para siempre, ni nadie las arrebatará de mi mano. (aiōn g165, aiōnios g166)
29 Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana.
Mi Padre que me [las] dió, mayor que todos es: y nadie [las] puede arrebatar de la mano de mi Padre.
30 Da ni da Uba ɗaya ne.”
Yo y el Padre una cosa somos.
31 Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi,
Entónces volvieron á tomar piedras los Judíos para apedrearle.
32 amma Yesu ya ce musu, “Na nuna muku ayyukan alheri masu yawa da Uba ya aiko ni in yi, a kan wanne kuke so ku jajjefe ni?”
Respondióles Jesus: Muchas buenas obras os he mostrado de mi Padre, ¿por cuál obra de esas me apedreais?
33 Yahudawa suka amsa suka ce, “Ai, ba don wani daga cikin waɗannan ayyukan alheri ne muke so mu jajjefe ka ba, amma don saɓon da kake yi, kai da kake mutum kawai, kana mai da kanka Allah.”
Respondiéronle los Judíos, diciendo: Por buena obra no te apedreamos sino por la blasfemia; y porque tú, siendo hombre, te haces Dios.
34 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a cikin Dokarku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’?
Respondióles Jesus: ¿No está escrito en vuestra ley: Yo dije: Dioses sois?
35 Mun dai san Nassi ba ya ƙarya, In har ya kira su waɗanda maganar Allah ta zo musu, ‘alloli,’
Si dijo dioses á aquellos, á los cuales fué hecha palabra de Dios, y la escritura no puede ser quebrantada:
36 to, game da wanda Uba ya keɓe a matsayin nasa ne ya kuma aiko shi duniya. Don me kuke ce saɓo nake, domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’
¿A [mí á] quien el Padre santificó, y envió al mundo, vosotros decís: Tú blasfemas; porque dije: Hijo de Dios soy?
37 In ba ayyukan da Ubana yake yi ne nake yi ba, to, kada ku gaskata ni.
Si no hago obras de mi Padre, no me creais.
38 Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.”
Mas si [las] hago, aunque á mí no creais, creed á las obras, para que conozcais y creais que el Padre está en mí, y yo en el Padre.
39 Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.
Y procuraban otra vez prenderle; mas él se salió de sus manos.
40 Sa’an nan Yesu ya sāke koma ƙetaren Urdun inda dā Yohanna yake baftisma. A can ya zauna
Y volvióse tras el Jordan, á aquel lugar donde primero habia estado bautizando Juan, y estúvose allí.
41 mutane da yawa suka zo wurinsa. Suka ce, “Ko da yake Yohanna bai yi wani abin banmamaki ba, duk abubuwan da Yohanna ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.”
Y muchos venian á él, y decian: Juan á la verdad ninguna señal hizo; mas todo lo que Juan dijo de este era verdad.
42 A nan kuwa mutane da yawa suka gaskata da Yesu.
Y muchos creyeron allí en él.

< Yohanna 10 >