< Yohanna 10 >

1 “Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma.
Verily, verily, I say unto you: —He that entereth not, through the door, into the fold of the sheep, but goeth up from another place, that man, is, a thief, and, a robber.
2 Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne.
But, he that entereth through the door, is, shepherd, of the sheep:
3 Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje.
To him, the porter openeth, and, the sheep, unto his voice, hearken: and, his own sheep, he calleth by name, and leadeth them forth.
4 Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa.
As soon as, all his own, he hath put forth, before them, he moveth on, and, the sheep, follow him, because they know his voice;
5 Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.”
But, a stranger, will they in nowise follow, but will flee from him, because they know not the voice, of strangers.
6 Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.
This similitude, spake Jesus unto them; but, those men, understood not what the things were which he was speaking unto them.
7 Saboda haka Yesu ya sāke cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ni ne ƙofar tumakin.
Jesus, therefore, said, again—Verily, verily, I say unto you: —I, am the door of the sheep:
8 Duk waɗanda suka riga ni zuwa ɓarayi ne,’yan fashi kuma, amma tumakin ba su saurare su ba.
All, as many as came before me, are thieves, and, robbers: but the sheep hearkened nor unto them.
9 Ni ne ƙofar; duk wanda ya shiga ta wurina zai sami ceto. Zai riƙa shiga yă fita yă kuwa sami wurin kiwo.
I, am the door: through me, if anyone enter, he shall be saved, and shall come in and go out, and, pasture, shall find.
10 Ɓarawo yakan zo don yă yi sata ne kawai da kisa da kuma ɓarna. Ni kuwa na zo ne don su sami rai, su kuma same shi a yalwace.
The thief, cometh not, save that he may thieve and slay and destroy: I, came, that, life, they might have, and, above measure, might have.
11 “Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yakan ba da ransa domin tumakin.
I, am the good shepherd: The good shepherd, his life, layeth down, for the sheep.
12 Wanda aka ɗauko haya ba shi ne makiyayi mai tumakin ba. Saboda haka sa’ad da ya ga kyarkeci yana zuwa, sai yă sheƙa da gudu yă bar tumakin. Sai kyarkecin yă kai wa garken hari, yă kuma watsar da su.
The hireling, even because he is no shepherd, whose own the sheep are not, vieweth the wolf coming, and leaveth the sheep, and fleeth, —and, the wolf, seizeth them and scattereth, —
13 Mutumin yakan gudu don shi ɗan haya ne kawai, bai kuwa damu da tumakin ba.
Because, a hireling, he is, and hath no care for the sheep.
14 “Ni ne makiyayi mai kyau; na san tumakina, tumakina kuma sun san ni,
I, am the good shepherd, and know my own, and, my own, know me, —
15 kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uba, ina kuwa ba da raina domin tumakin.
Just as, the Father, knoweth me, and, I, know, the Father; and, my life, I lay down for the sheep.
16 Ina da waɗansu tumaki da ba na wannan garken ba ne. Dole ne in kawo su su ma. Za su saurari muryata, za su kasance garke guda ɗaya, makiyayi guda kuma.
And, other sheep, have I, which are not of this fold: those also, I must needs bring, and, unto my voice, will they hearken, and there shall come to be, One flock, One shepherd.
17 Abin da ya sa Ubana yake ƙaunata ke nan, domin ina ba da raina, in ɗauko shi kuma.
Therefore, doth the Father, love, me, because, I, lay down my life, that, again, I may receive it: —
18 Ba mai karɓe mini rai, ina dai ba da shi. Ina da iko in ba da shi, ina da iko in ɗauko shi kuma. Wannan umarni kuwa daga wurin Ubana na karɓo shi.”
No one, forced it from me, but, I, lay it down, of myself, —Authority, have I, to lay it down, and, authority, have I, again, to receive it: This commandment, received I, from my Father.
19 Saboda waɗannan kalmomi fa, sai ɓaraka ta sāke shiga cikin Yahudawa.
A division, again, took place among the Jews, because of these words.
20 Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”
But many from among them were saying—A demon, he hath, and is raving, —Why, unto him, do ye hearken?
21 Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
Others, said—These sayings, are not those of one demonized, —Can, a demon, open the eyes of, the blind?
22 Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
The feast of dedication took place at that time, in Jerusalem: it was, winter,
23 Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
and Jesus was walking in the temple, in the porch of Solomon.
24 sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
The Jews, therefore, surrounded him, and were saying unto him—How long, holdest thou, our lives, in suspense? If, thou, art the Christ, tell us, plainly.
25 Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
Jesus answered them—I told you, and ye believe not: The works which, I, am doing in the name of my Father, the same, bear witness concerning me.
26 Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
But, ye, believe not, because ye are not of my sheep.
27 Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
My sheep, unto my voice, hearken, —and, I, know, them, and they follow me, —
28 Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn g165, aiōnios g166)
And, I, give unto them life age-abiding, and in nowise shall they perish, unto times age-abiding; and no one shall carry them off out of my hand. (aiōn g165, aiōnios g166)
29 Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana.
What, my Father, hath given me, is, something greater than all, and, no one, can carry off out of the hand of my Father: —
30 Da ni da Uba ɗaya ne.”
I and the Father, are, one.
31 Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi,
The Jews again lifted up stones, that they might stone him.
32 amma Yesu ya ce musu, “Na nuna muku ayyukan alheri masu yawa da Uba ya aiko ni in yi, a kan wanne kuke so ku jajjefe ni?”
Jesus answered them—Many works, have I showed you, noble ones, from my Father: For which of those works are ye stoning me?
33 Yahudawa suka amsa suka ce, “Ai, ba don wani daga cikin waɗannan ayyukan alheri ne muke so mu jajjefe ka ba, amma don saɓon da kake yi, kai da kake mutum kawai, kana mai da kanka Allah.”
The Jews answered him—Concerning a noble work, are we not stoning thee; but concerning profane speech, —and because, thou, being, a man, art making thyself, God.
34 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a cikin Dokarku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’?
Jesus answered them—Is it not written in your law: I, said, Ye are, gods?
35 Mun dai san Nassi ba ya ƙarya, In har ya kira su waɗanda maganar Allah ta zo musu, ‘alloli,’
If, those, he called gods, unto whom, the word of God, came—and the Scripture cannot be broken—
36 to, game da wanda Uba ya keɓe a matsayin nasa ne ya kuma aiko shi duniya. Don me kuke ce saɓo nake, domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’
Of him whom, the Father, hallowed and sent forth into the world, are, ye, saying—Thou speakest profanely, because I said, Son of God, I am?
37 In ba ayyukan da Ubana yake yi ne nake yi ba, to, kada ku gaskata ni.
If I am not doing the works of my Father, do not believe in me;
38 Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.”
But, if I am doing them, even though, in me, ye believe not, in the works, believe, —that ye may get to know and go on to know, that the Father is, in me, and, I, am, in the Father.
39 Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.
They were [therefore] again seeking to take him; and he went forth out of their hand.
40 Sa’an nan Yesu ya sāke koma ƙetaren Urdun inda dā Yohanna yake baftisma. A can ya zauna
And he went away again, beyond the Jordan, unto the place where John was at the first, immersing; and he abode there.
41 mutane da yawa suka zo wurinsa. Suka ce, “Ko da yake Yohanna bai yi wani abin banmamaki ba, duk abubuwan da Yohanna ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.”
And, many, came unto him, and were saying—John, indeed, did not so much as, one sign; but, all things, whatsoever John said concerning this one, were, true.
42 A nan kuwa mutane da yawa suka gaskata da Yesu.
And, many, believed on him there.

< Yohanna 10 >