< Yohanna 10 >

1 “Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma.
Verely, verely I say vnto you, Hee that entreth not in by the doore into the sheepefolde, but climeth vp another way, he is a theefe and a robber.
2 Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne.
But he that goeth in by the doore, is the shepheard of the sheepe.
3 Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje.
To him the porter openeth, and the sheepe heare his voyce, and he calleth his owne sheepe by name, and leadeth them out.
4 Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa.
And when hee hath sent foorth his owne sheepe, he goeth before them, and the sheepe follow him: for they know his voyce.
5 Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.”
And they will not follow a stranger, but they flee from him: for they know not the voyce of strangers.
6 Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.
This parable spake Iesus vnto them: but they vnderstoode not what things they were which he spake vnto them.
7 Saboda haka Yesu ya sāke cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ni ne ƙofar tumakin.
Then sayd Iesus vnto them againe, Verely, verely I say vnto you, I am that doore of the sheepe.
8 Duk waɗanda suka riga ni zuwa ɓarayi ne,’yan fashi kuma, amma tumakin ba su saurare su ba.
All, that euer came before me, are theeues and robbers: but the sheepe did not heare them.
9 Ni ne ƙofar; duk wanda ya shiga ta wurina zai sami ceto. Zai riƙa shiga yă fita yă kuwa sami wurin kiwo.
I am that doore: by me if any man enter in, he shall be saued, and shall go in, and go out, and finde pasture.
10 Ɓarawo yakan zo don yă yi sata ne kawai da kisa da kuma ɓarna. Ni kuwa na zo ne don su sami rai, su kuma same shi a yalwace.
The theefe commeth not, but for to steale, and to kill, and to destroy: I am come that they might haue life, and haue it in abundance.
11 “Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yakan ba da ransa domin tumakin.
I am that good shepheard: that good shepheard giueth his life for his sheepe.
12 Wanda aka ɗauko haya ba shi ne makiyayi mai tumakin ba. Saboda haka sa’ad da ya ga kyarkeci yana zuwa, sai yă sheƙa da gudu yă bar tumakin. Sai kyarkecin yă kai wa garken hari, yă kuma watsar da su.
But an hireling, and hee which is not the shepheard, neither the sheepe are his owne, seeth the wolfe comming, and hee leaueth the sheepe, and fleeth, and the wolfe catcheth them, and scattreth the sheepe.
13 Mutumin yakan gudu don shi ɗan haya ne kawai, bai kuwa damu da tumakin ba.
So the hireling fleeth, because he is an hireling, and careth not for the sheepe.
14 “Ni ne makiyayi mai kyau; na san tumakina, tumakina kuma sun san ni,
I am that good shepheard, and knowe mine, and am knowen of mine.
15 kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uba, ina kuwa ba da raina domin tumakin.
As the Father knoweth me, so know I the Father: and I lay downe my life for my sheepe.
16 Ina da waɗansu tumaki da ba na wannan garken ba ne. Dole ne in kawo su su ma. Za su saurari muryata, za su kasance garke guda ɗaya, makiyayi guda kuma.
Other sheepe I haue also, which are not of this folde: them also must I bring, and they shall heare my voyce: and there shalbe one sheepefolde, and one shepheard.
17 Abin da ya sa Ubana yake ƙaunata ke nan, domin ina ba da raina, in ɗauko shi kuma.
Therefore doeth my Father loue me, because I lay downe my life, that I might take it againe.
18 Ba mai karɓe mini rai, ina dai ba da shi. Ina da iko in ba da shi, ina da iko in ɗauko shi kuma. Wannan umarni kuwa daga wurin Ubana na karɓo shi.”
No man taketh it from me, but I lay it downe of my selfe: I haue power to lay it downe, and haue power to take it againe: this commandement haue I receiued of my Father.
19 Saboda waɗannan kalmomi fa, sai ɓaraka ta sāke shiga cikin Yahudawa.
Then there was a dissension againe among the Iewes for these sayings,
20 Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”
And many of them sayd, He hath a deuill, and is mad: why heare ye him?
21 Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
Other sayd, These are not the wordes of him that hath a deuill: can the deuill open the eyes of the blinde?
22 Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
And it was at Hierusalem the feast of the Dedication, and it was winter.
23 Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
And Iesus walked in the Temple, in Salomons porche.
24 sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
Then came the Iewes round about him, and sayd vnto him, Howe long doest thou make vs dout? If thou be that Christ, tell vs plainely.
25 Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
Iesus answered them, I tolde you, and ye beleeue not: the workes that I doe in my Fathers Name, they beare witnes of me.
26 Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
But ye beleeue not: for ye are not of my sheepe, as I sayd vnto you.
27 Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
My sheepe heare my voyce, and I knowe them, and they follow me,
28 Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn g165, aiōnios g166)
And I giue vnto them eternall life, and they shall neuer perish, neither shall any plucke them out of mine hand. (aiōn g165, aiōnios g166)
29 Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana.
My Father which gaue them me, is greater then all, and none is able to take them out of my Fathers hand.
30 Da ni da Uba ɗaya ne.”
I and my Father are one.
31 Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi,
Then ye Iewes againe tooke vp stones, to stone him.
32 amma Yesu ya ce musu, “Na nuna muku ayyukan alheri masu yawa da Uba ya aiko ni in yi, a kan wanne kuke so ku jajjefe ni?”
Iesus answered them, Many good workes haue I shewed you from my Father: for which of these workes doe ye stone me?
33 Yahudawa suka amsa suka ce, “Ai, ba don wani daga cikin waɗannan ayyukan alheri ne muke so mu jajjefe ka ba, amma don saɓon da kake yi, kai da kake mutum kawai, kana mai da kanka Allah.”
The Iewes answered him, saying, For the good worke we stone thee not, but for blasphemie, and that thou being a man, makest thy selfe God.
34 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a cikin Dokarku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’?
Iesus answered them, Is it not written in your Lawe, I sayd, Ye are gods?
35 Mun dai san Nassi ba ya ƙarya, In har ya kira su waɗanda maganar Allah ta zo musu, ‘alloli,’
If hee called them gods, vnto whome the worde of God was giuen, and the Scripture cannot be broken,
36 to, game da wanda Uba ya keɓe a matsayin nasa ne ya kuma aiko shi duniya. Don me kuke ce saɓo nake, domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’
Say ye of him, whome the Father hath sanctified, and sent into the worlde, Thou blasphemest, because I said, I am the Sonne of God?
37 In ba ayyukan da Ubana yake yi ne nake yi ba, to, kada ku gaskata ni.
If I doe not the workes of my Father, beleeue me not.
38 Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.”
But if I doe, then though ye beleeue not mee, yet beleeue the workes, that ye may knowe and beleeue, that the Father is in me, and I in him.
39 Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.
Againe they went about to take him: but he escaped out of their handes,
40 Sa’an nan Yesu ya sāke koma ƙetaren Urdun inda dā Yohanna yake baftisma. A can ya zauna
And went againe beyonde Iordan, into the place where Iohn first baptized, and there abode.
41 mutane da yawa suka zo wurinsa. Suka ce, “Ko da yake Yohanna bai yi wani abin banmamaki ba, duk abubuwan da Yohanna ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.”
And many resorted vnto him, and saide, Iohn did no miracle: but all thinges that Iohn spake of this man, were true.
42 A nan kuwa mutane da yawa suka gaskata da Yesu.
And many beleeued in him there.

< Yohanna 10 >