< Yohanna 10 >
1 “Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma.
Amen, amen I say to you: He that entereth not by the door into the sheepfold, but climbeth up another way, the same is a thief and a robber.
2 Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne.
But he that entereth in by the door is the shepherd of the sheep.
3 Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje.
To him the porter openeth; and the sheep hear his voice: and he calleth his own sheep by name, and leadeth them out.
4 Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa.
And when he hath let out his own sheep, he goeth before them: and the sheep follow him, because they know his voice.
5 Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.”
But a stranger they follow not, but fly from him, because they know not the voice of strangers.
6 Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.
This proverb Jesus spoke to them. But they understood not what he spoke to them.
7 Saboda haka Yesu ya sāke cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ni ne ƙofar tumakin.
Jesus therefore said to them again: Amen, amen I say to you, I am the door of the sheep.
8 Duk waɗanda suka riga ni zuwa ɓarayi ne,’yan fashi kuma, amma tumakin ba su saurare su ba.
All others, as many as have come, are thieves and robbers: and the sheep heard them not.
9 Ni ne ƙofar; duk wanda ya shiga ta wurina zai sami ceto. Zai riƙa shiga yă fita yă kuwa sami wurin kiwo.
I am the door. By me, if any man enter in, he shall be saved: and he shall go in, and go out, and shall find pastures.
10 Ɓarawo yakan zo don yă yi sata ne kawai da kisa da kuma ɓarna. Ni kuwa na zo ne don su sami rai, su kuma same shi a yalwace.
The thief cometh not, but for to steal, and to kill, and to destroy. I am come that they may have life, and may have it more abundantly.
11 “Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yakan ba da ransa domin tumakin.
I am the good shepherd. The good shepherd giveth his life for his sheep.
12 Wanda aka ɗauko haya ba shi ne makiyayi mai tumakin ba. Saboda haka sa’ad da ya ga kyarkeci yana zuwa, sai yă sheƙa da gudu yă bar tumakin. Sai kyarkecin yă kai wa garken hari, yă kuma watsar da su.
But the hireling, and he that is not the shepherd, whose own the sheep are not, seeth the wolf coming, and leaveth the sheep, and flieth: and the wolf catcheth, and scattereth the sheep:
13 Mutumin yakan gudu don shi ɗan haya ne kawai, bai kuwa damu da tumakin ba.
And the hireling flieth, because he is a hireling: and he hath no care for the sheep.
14 “Ni ne makiyayi mai kyau; na san tumakina, tumakina kuma sun san ni,
I am the good shepherd; and I know mine, and mine know me.
15 kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uba, ina kuwa ba da raina domin tumakin.
As the Father knoweth me, and I know the Father: and I lay down my life for my sheep.
16 Ina da waɗansu tumaki da ba na wannan garken ba ne. Dole ne in kawo su su ma. Za su saurari muryata, za su kasance garke guda ɗaya, makiyayi guda kuma.
And other sheep I have, that are not of this fold: them also I must bring, and they shall hear my voice, and there shall be one fold and one shepherd.
17 Abin da ya sa Ubana yake ƙaunata ke nan, domin ina ba da raina, in ɗauko shi kuma.
Therefore doth the Father love me: because I lay down my life, that I may take it again.
18 Ba mai karɓe mini rai, ina dai ba da shi. Ina da iko in ba da shi, ina da iko in ɗauko shi kuma. Wannan umarni kuwa daga wurin Ubana na karɓo shi.”
No man taketh it away from me: but I lay it down of myself, and I have power to lay it down: and I have power to take it up again. This commandment have I received of my Father.
19 Saboda waɗannan kalmomi fa, sai ɓaraka ta sāke shiga cikin Yahudawa.
A dissension rose again among the Jews for these words.
20 Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”
And many of them said: He hath a devil, and is mad: why hear you him?
21 Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
Others said: These are not the words of one that hath a devil: Can a devil open the eyes of the blind?
22 Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
And it was the feast of the dedication at Jerusalem: and it was winter.
23 Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
And Jesus walked in the temple, in Solomon’s porch.
24 sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
The Jews therefore came round about him, and said to him: How long dost thou hold our souls in suspense? If thou be the Christ, tell us plainly.
25 Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
Jesus answered them: I speak to you, and you believe not: the works that I do in the name of my Father, they give testimony of me.
26 Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
But you do not believe, because you are not of my sheep.
27 Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
My sheep hear my voice: and I know them, and they follow me.
28 Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn , aiōnios )
And I give them life everlasting; and they shall not perish for ever, and no man shall pluck them out of my hand. (aiōn , aiōnios )
29 Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana.
That which my Father hath given me, is greater than all: and no one can snatch them out of the hand of my Father.
30 Da ni da Uba ɗaya ne.”
I and the Father are one.
31 Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi,
The Jews then took up stones to stone him.
32 amma Yesu ya ce musu, “Na nuna muku ayyukan alheri masu yawa da Uba ya aiko ni in yi, a kan wanne kuke so ku jajjefe ni?”
Jesus answered them: Many good works I have shewed you from my Father; for which of these works do you stone me?
33 Yahudawa suka amsa suka ce, “Ai, ba don wani daga cikin waɗannan ayyukan alheri ne muke so mu jajjefe ka ba, amma don saɓon da kake yi, kai da kake mutum kawai, kana mai da kanka Allah.”
The Jews answered him: For a good work we stone thee not, but for blasphemy; and because that thou, being a man, maketh thyself God.
34 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a cikin Dokarku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’?
Jesus answered them: Is it not written in your law: I said you are gods?
35 Mun dai san Nassi ba ya ƙarya, In har ya kira su waɗanda maganar Allah ta zo musu, ‘alloli,’
If he called them gods, to whom to word of God was spoken, and the scripture cannot be broken;
36 to, game da wanda Uba ya keɓe a matsayin nasa ne ya kuma aiko shi duniya. Don me kuke ce saɓo nake, domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’
Do you say of him whom the Father hath sanctified and sent into the world: Thou blasphemest, because I said, I am the Son of God?
37 In ba ayyukan da Ubana yake yi ne nake yi ba, to, kada ku gaskata ni.
If I do not the works of my Father, believe me not.
38 Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.”
But if I do, though you will not believe me, believe the works: that you may know and believe that the Father is in me, and I in the Father.
39 Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.
They sought therefore to take him; and he escaped out of their hands.
40 Sa’an nan Yesu ya sāke koma ƙetaren Urdun inda dā Yohanna yake baftisma. A can ya zauna
And he went again beyond the Jordan, into that place where John was baptizing first; and there he abode.
41 mutane da yawa suka zo wurinsa. Suka ce, “Ko da yake Yohanna bai yi wani abin banmamaki ba, duk abubuwan da Yohanna ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.”
And many resorted to him, and they said: John indeed did no sign.
42 A nan kuwa mutane da yawa suka gaskata da Yesu.
But all things whatsoever John said of this man, were true. And many believed in him.