< Yohanna 10 >
1 “Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma.
Verily, verily I say to you, he that goes not through the door into the sheepfold, but climbs up some other way, he is a thief, and a robber.
2 Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne.
But he that enters through the door, is the shepherd of the sheep.
3 Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje.
To him the door-keeper opens; and the sheep hear his voice, and he calls his own sheep by name, and leads them out.
4 Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa.
And when he puts his own sheep out, he goes before them; and the sheep follow him; for they know his voice.
5 Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.”
And a stranger they will not follow, but will flee from him; for they know not the voice of strangers.
6 Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.
This parable spoke Jesus to them; but they knew not the meaning of the things which he spoke to them.
7 Saboda haka Yesu ya sāke cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ni ne ƙofar tumakin.
Therefore Jesus spoke again to them: Verily, verily I say to you, I am the door of the sheep.
8 Duk waɗanda suka riga ni zuwa ɓarayi ne,’yan fashi kuma, amma tumakin ba su saurare su ba.
All that came before me were thieves and robbers; but the sheep did not hear them.
9 Ni ne ƙofar; duk wanda ya shiga ta wurina zai sami ceto. Zai riƙa shiga yă fita yă kuwa sami wurin kiwo.
I am the door: if any one enters through me, he shall be saved; and he shall go in and out, and find pasture.
10 Ɓarawo yakan zo don yă yi sata ne kawai da kisa da kuma ɓarna. Ni kuwa na zo ne don su sami rai, su kuma same shi a yalwace.
The thief comes only to steal and kill and destroy. I have come that they may have life, and have it in abundance.
11 “Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yakan ba da ransa domin tumakin.
I am the good shepherd: the good shepherd lays down his life for the sheep.
12 Wanda aka ɗauko haya ba shi ne makiyayi mai tumakin ba. Saboda haka sa’ad da ya ga kyarkeci yana zuwa, sai yă sheƙa da gudu yă bar tumakin. Sai kyarkecin yă kai wa garken hari, yă kuma watsar da su.
But he that is a hireling, and not the shepherd, to whom the sheep do not belong, sees the wolf coming, and leaves the sheep, and flees; and the wolf catches the sheep, and scatters them.
13 Mutumin yakan gudu don shi ɗan haya ne kawai, bai kuwa damu da tumakin ba.
The hireling flees because he is a hireling, and cares not for the sheep.
14 “Ni ne makiyayi mai kyau; na san tumakina, tumakina kuma sun san ni,
I am the good shepherd, and I know my sheep, and am known by mine.
15 kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uba, ina kuwa ba da raina domin tumakin.
As the Father knows me, I also know the Father, and I lay down my life for the sheep.
16 Ina da waɗansu tumaki da ba na wannan garken ba ne. Dole ne in kawo su su ma. Za su saurari muryata, za su kasance garke guda ɗaya, makiyayi guda kuma.
And other sheep I have, which are not of this fold; those, also, must I bring, and they will hear my voice: and there shall be one flock, one shepherd.
17 Abin da ya sa Ubana yake ƙaunata ke nan, domin ina ba da raina, in ɗauko shi kuma.
For this reason, my Father loves me, because I lay down my life that I may take it again.
18 Ba mai karɓe mini rai, ina dai ba da shi. Ina da iko in ba da shi, ina da iko in ɗauko shi kuma. Wannan umarni kuwa daga wurin Ubana na karɓo shi.”
No one takes it from me, but I lay it down of myself. I have authority to lay it down, and I have authority to take it again. This commandment I have received from my Father.
19 Saboda waɗannan kalmomi fa, sai ɓaraka ta sāke shiga cikin Yahudawa.
Again, therefore, there was a division among the Jews, on account of these words.
20 Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”
And many of them said: He has a demon, and is mad; why do you hear him?
21 Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
Others said: These are not the words of one that has a demon. Can a demon open the eyes of the blind?
22 Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
And the feast of the dedication was celebrated in Jerusalem, and it was winter:
23 Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
and Jesus was walking in the temple, in Solomon’s porch.
24 sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
Then the Jews came round him, and said to him: How long do you keep us in suspense? If you are the Christ, tell us plainly.
25 Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
Jesus answered them: I have told you, and you do not believe. The works which I do in my Father’s name, these testify of me.
26 Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
But you believe not, because you are not of my sheep. As I said to you,
27 Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
my sheep hear my voice, and I know them, and they follow me:
28 Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn , aiōnios )
and I give them eternal life; and they shall never perish, and no one shall take them out of my hand. (aiōn , aiōnios )
29 Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana.
My Father, who gave them to me, is greater than all; and no one is able to take them out of my Father’s hand.
30 Da ni da Uba ɗaya ne.”
I and my Father are one.
31 Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi,
Then the Jews took up stones again, to stone him.
32 amma Yesu ya ce musu, “Na nuna muku ayyukan alheri masu yawa da Uba ya aiko ni in yi, a kan wanne kuke so ku jajjefe ni?”
Jesus answered them: Many good works have I showed you from my Father: for which of these works do you stone me?
33 Yahudawa suka amsa suka ce, “Ai, ba don wani daga cikin waɗannan ayyukan alheri ne muke so mu jajjefe ka ba, amma don saɓon da kake yi, kai da kake mutum kawai, kana mai da kanka Allah.”
The Jews answered and said to him: We do not stone you for a good work, but for your impious words; and because you, being man, make yourself God.
34 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a cikin Dokarku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’?
Jesus answered them: Is it not written in your law, I said, you are gods?
35 Mun dai san Nassi ba ya ƙarya, In har ya kira su waɗanda maganar Allah ta zo musu, ‘alloli,’
If he called them gods, to whom the word of God was committed, (and the scripture can not be made void, )
36 to, game da wanda Uba ya keɓe a matsayin nasa ne ya kuma aiko shi duniya. Don me kuke ce saɓo nake, domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’
do you say of him, whom the Father has sanctified, and sent into the world, You speak impiously, because I said, I am the Son of God?
37 In ba ayyukan da Ubana yake yi ne nake yi ba, to, kada ku gaskata ni.
If I do not the works of my Father, believe me not;
38 Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.”
but if I do, though you believe not me, believe the works, that you may know and believe that the Father is in me, and I in him.
39 Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.
Then they sought again to take him, but he escaped from their hands.
40 Sa’an nan Yesu ya sāke koma ƙetaren Urdun inda dā Yohanna yake baftisma. A can ya zauna
And he went away again beyond the Jordan, to the place where John first immersed, and there he abode.
41 mutane da yawa suka zo wurinsa. Suka ce, “Ko da yake Yohanna bai yi wani abin banmamaki ba, duk abubuwan da Yohanna ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.”
And many came to him, and said: John did no sign; but all things that John said of this man were true.
42 A nan kuwa mutane da yawa suka gaskata da Yesu.
And many who were there believed on him.