< Yohanna 10 >
1 “Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma.
„Sandelig, sandelig, siger jeg eder, den, som ikke gaar ind i Faarefolden gennem Døren, men stiger andensteds over, han er en Tyv og en Røver.
2 Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne.
Men den, som gaar ind igennem Døren, er Faarenes Hyrde.
3 Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje.
For ham lukker Dørvogteren op, og Faarene høre hans Røst; og han kalder sine egne Faar ved Navn og fører dem ud.
4 Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa.
Og naar han har ført alle sine egne Faar ud, gaar han foran dem; og Faarene følge ham, fordi de kende hans Røst.
5 Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.”
Men en fremmed ville de ikke følge, men de ville fly fra ham, fordi de ikke kende de fremmedes Røst.”
6 Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.
Denne Lignelse sagde Jesus til dem; men de forstode ikke, hvad det var, som han talte til dem.
7 Saboda haka Yesu ya sāke cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ni ne ƙofar tumakin.
Jesus sagde da atter til dem: „Sandelig, sandelig, siger jeg eder, jeg er Faarenes Dør.
8 Duk waɗanda suka riga ni zuwa ɓarayi ne,’yan fashi kuma, amma tumakin ba su saurare su ba.
Alle de, som ere komne før mig, ere Tyve og Røvere; men Faarene hørte dem ikke.
9 Ni ne ƙofar; duk wanda ya shiga ta wurina zai sami ceto. Zai riƙa shiga yă fita yă kuwa sami wurin kiwo.
Jeg er Døren; dersom nogen gaar ind igennem mig, han skal frelses; og han skal gaa ind og gaa ud og finde Føde.
10 Ɓarawo yakan zo don yă yi sata ne kawai da kisa da kuma ɓarna. Ni kuwa na zo ne don su sami rai, su kuma same shi a yalwace.
Tyven kommer ikke uden for at stjæle og slagte og ødelægge; jeg er kommen, for at de skulle have Liv og have Overflod.
11 “Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yakan ba da ransa domin tumakin.
Jeg er den gode Hyrde; den gode Hyrde sætter sit Liv til for Faarene.
12 Wanda aka ɗauko haya ba shi ne makiyayi mai tumakin ba. Saboda haka sa’ad da ya ga kyarkeci yana zuwa, sai yă sheƙa da gudu yă bar tumakin. Sai kyarkecin yă kai wa garken hari, yă kuma watsar da su.
Men Lejesvenden, som ikke er Hyrde, hvem Faarene ikke høre til, ser Ulven komme og forlader Faarene og flyr, og Ulven røver dem og adspreder dem,
13 Mutumin yakan gudu don shi ɗan haya ne kawai, bai kuwa damu da tumakin ba.
fordi han er en Lejesvend og ikke bryder sig om Faarene.
14 “Ni ne makiyayi mai kyau; na san tumakina, tumakina kuma sun san ni,
Jeg er den gode Hyrde, og jeg kender mine, og mine kende mig,
15 kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uba, ina kuwa ba da raina domin tumakin.
ligesom Faderen kender mig, og jeg kender Faderen; og jeg sætter mit Liv til for Faarene.
16 Ina da waɗansu tumaki da ba na wannan garken ba ne. Dole ne in kawo su su ma. Za su saurari muryata, za su kasance garke guda ɗaya, makiyayi guda kuma.
Og jeg har andre Faar, som ikke høre til denne Fold; ogsaa dem bør jeg føre, og de skulle høre min Røst; og der skal blive een Hjord, een Hyrde.
17 Abin da ya sa Ubana yake ƙaunata ke nan, domin ina ba da raina, in ɗauko shi kuma.
Derfor elsker Faderen mig, fordi jeg sætter mit Liv til for at tage det igen.
18 Ba mai karɓe mini rai, ina dai ba da shi. Ina da iko in ba da shi, ina da iko in ɗauko shi kuma. Wannan umarni kuwa daga wurin Ubana na karɓo shi.”
Ingen tager det fra mig, men jeg sætter det til af mig selv. Jeg har Magt til at sætte det til, og jeg har Magt til at tage det igen. Dette Bud modtog jeg af min Fader.”
19 Saboda waɗannan kalmomi fa, sai ɓaraka ta sāke shiga cikin Yahudawa.
Der blev atter Splid iblandt Jøderne for disse Ords Skyld.
20 Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”
Og mange af dem sagde: „Han er besat og raser, hvorfor høre I ham?”
21 Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
Andre sagde: „Dette er ikke Ord af en besat; mon en ond Aand kan aabne blindes Øjne?”
22 Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
Men Tempelvielsens Fest indtraf i Jerusalem. Det var Vinter;
23 Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
og Jesus gik omkring i Helligdommen, i Salomons Søjlegang.
24 sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
Da omringede Jøderne ham og sagde til ham: „Hvor længe holder du vor Sjæl i Uvished? Dersom du er Kristus, da sig os det rent ud!”
25 Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
Jesus svarede dem: „Jeg har sagt eder det, og I tro ikke. De Gerninger, som jeg gør i min Faders Navn, de vidne om mig;
26 Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
men I tro ikke, fordi I ikke ere af mine Faar.
27 Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
Mine Faar høre min Røst, og jeg kender dem, og de følge mig,
28 Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn , aiōnios )
og jeg giver dem et evigt Liv, og de skulle i al Evighed ikke fortabes, og ingen skal rive dem ud af min Haand. (aiōn , aiōnios )
29 Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana.
Min Fader, som har givet mig dem, er større end alle; og ingen kan rive noget af min Faders Haand.
30 Da ni da Uba ɗaya ne.”
Jeg og Faderen, vi ere eet.”
31 Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi,
Da toge Jøderne atter Stene op for at stene ham.
32 amma Yesu ya ce musu, “Na nuna muku ayyukan alheri masu yawa da Uba ya aiko ni in yi, a kan wanne kuke so ku jajjefe ni?”
Jesus svarede dem: „Mange gode Gerninger har jeg vist eder fra min Fader; for hvilken af disse Gerninger stene I mig?”
33 Yahudawa suka amsa suka ce, “Ai, ba don wani daga cikin waɗannan ayyukan alheri ne muke so mu jajjefe ka ba, amma don saɓon da kake yi, kai da kake mutum kawai, kana mai da kanka Allah.”
Jøderne svarede ham: „For en god Gerning stene vi dig ikke, men for Gudsbespottelse, og fordi du, som er et Menneske, gør dig selv til Gud.”
34 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a cikin Dokarku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’?
Jesus svarede dem: „Er der ikke skrevet i eders Lov: Jeg har sagt: I ere Guder?
35 Mun dai san Nassi ba ya ƙarya, In har ya kira su waɗanda maganar Allah ta zo musu, ‘alloli,’
Naar den nu har kaldt dem Guder, til hvem Guds Ord kom (og Skriften kan ikke rokkes),
36 to, game da wanda Uba ya keɓe a matsayin nasa ne ya kuma aiko shi duniya. Don me kuke ce saɓo nake, domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’
sige I da til den, hvem Faderen har helliget og sendt til Verden: Du taler bespotteligt, fordi jeg sagde: Jeg er Guds Søn?
37 In ba ayyukan da Ubana yake yi ne nake yi ba, to, kada ku gaskata ni.
Dersom jeg ikke gør min Faders Gerninger, saa tror mig ikke!
38 Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.”
Men dersom jeg gør dem, saa tror Gerningerne, om I end ikke ville tro mig, for at I kunne indse og erkende, at Faderen er i mig, og jeg i Faderen.”
39 Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.
De søgte da atter at gribe ham; og han undslap af deres Haand.
40 Sa’an nan Yesu ya sāke koma ƙetaren Urdun inda dā Yohanna yake baftisma. A can ya zauna
Og han drog atter bort hinsides Jordan til det Sted, hvor Johannes først døbte, og han blev der.
41 mutane da yawa suka zo wurinsa. Suka ce, “Ko da yake Yohanna bai yi wani abin banmamaki ba, duk abubuwan da Yohanna ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.”
Og mange kom til ham, og de sagde: „Johannes gjorde vel intet Tegn; men alt, hvad Johannes sagde om denne, var sandt.”
42 A nan kuwa mutane da yawa suka gaskata da Yesu.
Og mange troede paa ham der.