< Yohanna 1 >

1 Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
2 Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
The same was in the beginning with God.
3 Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
By Him were all things made, and without Him was not any one thing made that was made.
4 A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
In Him was life, and the life was the light of men.
5 Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
And the light shineth in darkness, and the darkness attained it not.
6 Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
There was a man sent from God, whose name was John:
7 Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
this man came for witness, that he might testify concerning the light, that through him all might believe.
8 Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
He was not that light, but was sent to bear witness of the light.
9 Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
The true light was that which enlightneth every man that cometh into the world.
10 Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
He was in the world, and the world was made by Him, and yet the world knew Him not:
11 Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
yea, He came to his own peculiar right, and even his own people received Him not.
12 Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
But as many as received Him, to them granted He the privilege to become the children of God, even to them that believe on his name;
13 ’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
who were born not of blood, nor of the will of the flesh, nor of the will of man, but of God.
14 Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
And the Word was made flesh, and dwelt among us, being full of grace and truth: and we beheld his glory, the glory as of the only-begotten of the Father.
15 (Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
Of Him did John bare witness, and publicly declared, saying, This was He of whom I spake, He that cometh after me is preferred before me; for He was before me.
16 Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
And of his fulness have we all received, even grace for grace.
17 Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
For the law was given by Moses, but grace and truth came by Jesus Christ:
18 Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
and though no one hath ever seen God, or can see Him: yet the only-begotten Son, who is in the bosom of the Father, hath made Him known.
19 To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
And this is the testimony of John, when the Jews sent from Jerusalem priests and Levites to ask him, Who art thou?
20 Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
he confessed, and denied not; but declared openly, I am not the Christ.
21 Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
And they asked him, What then? art thou Elias? And he said, I am not. Art thou a prophet? and he answered, No.
22 A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
Therefore said they unto him, Who art thou? that we may give an answer to them that sent us: What dost thou say of thy self?
23 Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
and he said, I am the voice of one crying in the wilderness, "Make straight the way of the Lord," according to Esaias the prophet.
24 To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
Now they that were sent, were of the pharisees:
25 suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
and they asked him, and said to him, Why then dost thou baptize, if thou art not the Christ, nor Elias, nor a prophet?
26 Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
John answered them, saying, I baptize with water: but there standeth one among you, whom ye know not;
27 Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
that cometh after me, but is preferred before me, the latchet of whose shoe I am not worthy to unloose.
28 Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
These things passed at Bethabara beyond Jordan, where John was baptizing.
29 Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
The next day John seeth Jesus coming towards him, and saith, Behold the Lamb of God that taketh away the sin of the world.
30 Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
This is He of whom I said, After me cometh a man, who is preferred before me: for He was before me.
31 Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
And I knew Him not: but therefore came I baptizing with water, that He might be made known to Israel.
32 Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
And John testified saying, I saw the Spirit descending like a dove from heaven, and it abode upon Him.
33 Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
And I knew Him not: but He that sent me to baptize with water, said unto me, Upon whom thou shalt see the Spirit descending and abiding on Him, the same is he that baptizeth with the Holy Spirit.
34 Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
And I saw it, and therefore testified that this is the Son of God.
35 Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
The day following John was standing, (and two of his disciples, )
36 Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
and looking upon Jesus as He was walking, he saith, "Behold the lamb of God."
37 Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
And when the two disciples heard what he said, they followed Jesus.
38 Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
And Jesus turning, and seeing them following Him, saith unto them, What do ye seek? They said unto Him, Rabbi (that is to say, Master, ) where is thine abode?
39 Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
He saith unto them, Come and see. And they came and saw where He dwelt, and abode with Him that day: and it was about the tenth hour.
40 Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
Now Andrew the brother of Simon Peter, was one of the two that heard what John said, and thereupon followed Jesus.
41 Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
He first meeteth with his own brother Simon, and telleth him, "We have found the Messiah, which is to say, the Christ."
42 Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
And Andrew brought him to Jesus: and Jesus looking at him said, Thou art Simon the son of Jonas, thou shalt be called Cephas; which is interpreted a stone.
43 Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
The day following Jesus had a mind to go out into Galilee, and meeting with Philip, saith unto him, Follow me.
44 Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
Now Philip was of Bethsaida the city of Andrew and Peter.
45 Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
Philip meeting Nathaniel, saith unto him, We have found Him, of whom Moses in the law, and of whom the prophets also wrote, Jesus of Nazareth, the son of Jeseph.
46 Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
And Nathaniel said unto him, Can any thing good come out of Nazareth? Philip replied, Come and see.
47 Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
And when Jesus saw Nathaniel coming towards Him, He saith concerning him, "Behold an Israelite indeed, in whom is no guile."
48 Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
Nathaniel saith unto Him, Whence knowest thou me? Jesus answered him, Before Philip called thee, I saw thee, when under the fig-tree.
49 Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
Nathaniel replied, Rabbi, thou art the Son of God; thou art the king of Israel.
50 Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
Jesus answered and said unto him, Because I told thee that I saw thee under the fig-tree, thou believest: thou shalt see greater things than these.
51 Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”
And He saith unto him, Verily verily I say unto you, Ye shall hereafter see heaven opened, and the angels of God ascending and descending upon the Son of man.

< Yohanna 1 >