< Yohanna 1 >

1 Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
2 Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
He was in the beginning with God.
3 Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
All things came into being through Him, and apart from Him nothing that exists came into being.
4 A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
In Him was Life, and that Life was the Light of men.
5 Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
The Light shines in the darkness, and the darkness has not overpowered it.
6 Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
There was a man sent from God, whose name was John.
7 Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
He came as a witness, in order that he might give testimony concerning the Light--so that all might believe through him.
8 Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
He was not the Light, but he existed that he might give testimony concerning the Light.
9 Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
The true Light was that which illumines every man by its coming into the world.
10 Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
He was in the world, and the world came into existence through Him, and the world did not recognize Him.
11 Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
He came to the things that were His own, and His own people gave Him no welcome.
12 Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
But all who have received Him, to them--that is, to those who trust in His name--He has given the privilege of becoming children of God;
13 ’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
who were begotten as such not by human descent, nor through an impulse of their own nature, nor through the will of a human father, but from God.
14 Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
And the Word came in the flesh, and lived for a time in our midst, so that we saw His glory--the glory as of the Father's only Son, sent from His presence. He was full of grace and truth.
15 (Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
John gave testimony concerning Him and cried aloud, saying, "This is He of whom I said, 'He who is coming after me has been put before me,' for He was before me."
16 Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
For He it is from whose fulness we have all received, and grace upon grace.
17 Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
For the Law was given through Moses; grace and truth came through Jesus Christ.
18 Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
No human eye has ever seen God: the only Son, who is in the Father's bosom--He has made Him known.
19 To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
This also is John's testimony, when the Jews sent to him a deputation of Priests and Levites from Jerusalem to ask him who he was.
20 Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
He avowed--he did not conceal the truth, but avowed, "I am not the Christ."
21 Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
"What then?" they inquired; "are you Elijah?" "I am not," he said. "Are you the Prophet?" "No," he answered.
22 A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
So they pressed the question. "Who are you?" they said--"that we may take an answer to those who sent us. What account do you give of yourself?"
23 Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
"I am the voice," he replied, "of one crying aloud, 'Make straight the Lord's way in the Desert,' fulfilling the words of the Prophet Isaiah."
24 To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
They were Pharisees who had been sent.
25 suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
Again they questioned him. "Why then do you baptize," they said, "if you are neither the Christ nor Elijah nor the Prophet?"
26 Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
"I baptize in water only," John answered, "but in your midst stands One whom you do not know--
27 Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
He who is to come after me, and whose sandal-strap I am not worthy to unfasten."
28 Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
This conversation took place at Bethany beyond the Jordan, where John was baptizing.
29 Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
The next day John saw Jesus coming towards him and exclaimed, "Look, that is the Lamb of God who is to take away the sin of the world!
30 Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
This is He about whom I said, 'After me is to come One who has been put before me, because He was before me.'
31 Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
I did not yet know Him; but that He may be openly shown to Israel is the reason why I have come baptizing in water."
32 Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
John also gave testimony by stating: "I have seen the Spirit coming down like a dove out of Heaven; and it remained upon Him.
33 Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
I did not yet know Him, but He who sent me to baptize in water said to me, "'The One on whom you see the Spirit coming down, and remaining, He it is who baptizes in the Holy Spirit.'
34 Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
"This I have seen, and I have become a witness that He is the Son of God."
35 Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
Again the next day John was standing with two of his disciples,
36 Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
when he saw Jesus passing by, and said, "Look! that is the Lamb of God!"
37 Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
The two disciples heard his exclamation, and they followed Jesus.
38 Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
Then Jesus turned round, and seeing them following He asked them, "What is your wish?" "Rabbi," they replied--'Rabbi' means 'Teacher' --"where are you staying?"
39 Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
"Come and you shall see," He said. So they went and saw where He was staying, and they remained and spent that day with Him. It was then about ten o'clock in the morning.
40 Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
Andrew, Simon Peter's brother, was one of the two who heard John's exclamation and followed Jesus.
41 Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
He first found his own brother Simon, and said to him, "We have found the Messiah!" --that is to say, the Anointed One.
42 Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
He brought him to Jesus. Jesus looked at him and said, "You are Simon, son of John: you shall be called Cephas" --that is to say, Peter (or 'Rock').
43 Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
The next day, having decided to leave Bethany and go into Galilee, Jesus found Philip, and invited him to follow Him.
44 Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
(Now Philip came from Bethsaida, the same town as Andrew and Peter.)
45 Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
Then Philip found Nathanael, and said to him, "We have found him about whom Moses in the Law wrote, as well as the Prophets--Jesus, the son of Joseph, a man of Nazareth."
46 Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
"Can anything good come out of Nazareth?" replied Nathanael. "Come and see," said Philip.
47 Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
Jesus saw Nathanael approaching, and said of him, "Look! here is a true Israelite, in whom there is no deceitfulness!"
48 Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
"How do you know me?" Nathanael asked. "Before Philip called you," said Jesus, "when you were under the fig-tree I saw you."
49 Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
"Rabbi," cried Nathanael, "you are the Son of God, you are Israel's King!"
50 Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
"Because I said to you, 'I saw you under the fig-tree,'" replied Jesus, "do you believe? You shall see greater things than that."
51 Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”
"I tell you all in most solemn truth," He added, "that you shall see Heaven opened wide, and God's angels going up, and coming down to the Son of Man."

< Yohanna 1 >