< Yowel 1 >
1 Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
Слово Господнє, що було до Йоі́ла, Петуїлового сина.
2 Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
„Послухайте це, ви старші́, і візьміть до вух, усі мешка́нці землі: чи бувало таке́ за днів ваших, або за днів ваших батьків?
3 Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
Оповіда́йте про це синам вашим, а ваші сини — своїм ді́тям, а їхні сини — поколі́нню насту́пному.
4 Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
„Що лишилось по гу́сені, — зже́рла те все сарана́, що ж зоста́лося по сарані́ — пожер ко́ник, а решту по ко́нику зжерла черва́“.
5 Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
Пробудіться, п'яни́ці, і плачте й ридайте за виногра́довим соком усі, хто вина напива́ється, бо ві́днятий він від уст ваших!
6 Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
Бо на Край Мій прийшов люд міцний й незчисле́нний, його зуби — як ле́в'ячі зуби, а па́ща його — як в леви́ці.
7 Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
Виноград Мій зробив він спусто́шенням, Моє ж фі́ґове дерево геть полама́в, доще́нту його оголи́в та й покинув, галу́зки його побіліли.
8 Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
Голоси́, як та дівчина, вере́тою опере́зана, за нарече́ним юна́цтва свого́.
9 Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
Жертва хлі́бна й жертва лита спини́лася в домі Господньому, впали в жало́бу священики, слу́ги Господні.
10 Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
Опусто́шене поле, упала в жало́бу земля, бо спусто́шене збіжжя, вино молоде пересо́хло, зів'я́ла оливка.
11 Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
Засоро́милися рільники́, голосили були виногра́дарі за пшеницю й ячмі́нь, бо ви́гинуло жниво поля.
12 Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
Усох виноград, а фіґа зів'я́ла, грана́тове дерево, й па́льма та яблуня, і повсиха́ли всі пі́льні дере́ва, бо Він висушив радість від лю́дських синів.
13 Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
Опережіться веретою, — і ридайте, священики, голосіть, слуги же́ртівника, входьте, ночуйте в вере́тах, служителі Бога мого́, — бо хлі́бна жертва і жертва та лита затри́мана бу́де від дому вашого Бога!
14 Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
Оголосіть святий піст, скличте збори, позбирайте старши́х, всіх мешка́нців землі до дому Господа, вашого Бога, і кли́чте до Господа.
15 Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
Горе дневі тому́! Бо близьки́й день Господній, і при́йде він від Всемогу́тнього, мов те спусто́шення!
16 Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
Чи ж з-перед оче́й наших не відіймається ї́жа, з дому нашого Бога веселість та втіха?
17 Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
Поко́рчились зе́рна під своїми гру́дами, спорожні́ли комо́ри, поруйно́вані клу́ні, бо висохло збі́жжя.
18 Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
Як стогне това́р, поголо́мшені че́реди, — бо немає їм па́ші, ота́ри спусто́шені!
19 A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
До тебе я кли́чу, о Господи, пожер бо огонь пасови́ща пустині, а жар попали́в усі дере́ва на полі.
20 Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.
Навіть пі́льна худо́ба пра́гне до Тебе, бо водні джере́ла посо́хли, огонь же поже́р пасови́ща пустині!