< Yowel 1 >

1 Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
Herrens ord som kom til Joel, Petuels sønn:
2 Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
Hør dette, I gamle! Gi akt, alle som bor i landet! Er sådant skjedd i eders dager eller i eders fedres dager?
3 Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
I skal fortelle om det til eders barn, og eders barn til sine barn, og deres barn til en kommende slekt.
4 Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
Hvad gnageren har levnet, har vrimleren ett, og hvad vrimleren har levnet, har slikkeren ett, og hvad slikkeren har levnet, har skaveren ett.
5 Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
Våkn op, I drukne, og gråt, og jamre, alle vindrikkere, fordi mosten er revet bort fra eders munn.
6 Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
For et folk har draget op over mitt land sterkt og talløst; dets tenner er som en løves tenner, og det har jeksler som en løvinne.
7 Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
Det har rent ødelagt mine vintrær og knekket mine fikentrær; det har gjort dem aldeles bare og kastet dem bort; deres grener er blitt hvite.
8 Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
Klag som en jomfru som bærer sørgedrakt for sin ungdoms brudgom!
9 Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
Matoffer og drikkoffer er revet bort fra Herrens hus; prestene, Herrens tjenere, sørger.
10 Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
Marken er ødelagt, jorden sørger; for kornet er ødelagt, mosten er tørket bort, oljen er svunnet inn.
11 Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
Akerdyrkerne er skuffet, vingårdsmennene jamrer sig; for hveten og bygget, markens grøde, er gått tapt.
12 Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
Vintreet er tørket bort, og fikentreet er visnet; granatepletreet og palmen og epletreet, alle markens trær er tørket bort; ja, all fryd er svunnet bort fra menneskenes barn.
13 Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
Klæ eder i sørgedrakt og klag, I prester! Jamre eder, I som gjør tjeneste ved alteret! Gå inn og sitt hele natten i sørgedrakt, I min Guds tjenere! For eders Guds hus må savne matoffer og drikkoffer.
14 Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
Tillys en hellig faste, utrop en festforsamling, samle de eldste, ja alle som bor i landet, til Herrens, eders Guds hus og rop til Herren!
15 Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
Ve oss, for en dag! For Herrens dag er nær og kommer som en ødeleggelse fra den Allmektige.
16 Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
Er ikke maten blitt borte for våre øine, glede og fryd fra vår Guds hus?
17 Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
Sædekornene er tørket inn under mulden som dekker dem; forrådshusene er ødelagt, ladene nedbrutt, for kornet er fordervet.
18 Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
Hvor buskapen stønner! Oksehjordene farer redde omkring, for det finnes intet beite for dem; også fårehjordene må lide.
19 A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
Til dig, Herre, roper jeg; for ild har fortært ørkenens beitemarker, og luer har forbrent alle markens trær.
20 Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.
Endog markens dyr skriker op til dig; for bekkene er uttørket, og ild har fortært ørkenens beitemarker.

< Yowel 1 >