< Yowel 1 >
1 Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
[the] word of Yahweh which it came to Joel [the] son of Pethuel.
2 Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
Hear this O elders and give ear O all [the] inhabitants of the land ¿ has it happened this in days your and or? in [the] days of ancestors your.
3 Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
On it to children your recount and children your to children their and children their to a generation another.
4 Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
[the] remainder of The locust[s] it has eaten the locust[s] and [the] remainder of the locust[s] it has eaten the locust[s] and [the] remainder of the locust[s] it has eaten the locust[s].
5 Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
Awake O drunkards and weep and wail O all drinkers of wine on sweet wine for it has been cut off from mouth your.
6 Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
For a nation it has come up on land my mighty and there not [is] number teeth its [are the] teeth of a lion and [the] fangs of a lioness [belong] to it.
7 Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
It has made vine[s] my into a waste and fig tree[s] my into a stump completely it has stripped bare it and it has thrown [it] away they have become white branches its.
8 Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
Wail like a virgin girded of sackcloth on [the] husband of youth her.
9 Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
It has been cut off grain offering and drink offering from [the] house of Yahweh they are in mourning the priests [the] servants of Yahweh.
10 Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
It is devastated [the] field[s] it is dried up [the] ground for it is devastated [the] grain it has dried up [the] new wine it has dried out [the] fresh oil.
11 Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
Be ashamed O farmers wail O vinedressers on [the] wheat and on [the] barley for it has perished [the] harvest of [the] field.
12 Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
The vine it has dried up and the fig tree it has dried out [the] pomegranate tree also [the] palm tree and [the] apple tree all [the] trees of the field they have dried up for it has been ashamed joy from [the] children of humankind.
13 Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
Gird yourselves and lament O priests wail O servants of [the] altar come spend [the] night in sackcloth O servants of God my for it has been withheld from [the] house of God your grain offering and drink offering.
14 Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
Consecrate a fast call an assembly gather [the] elders all [the] inhabitants of the land [the] house of Yahweh God your and cry out to Yahweh.
15 Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
Alas! for the day for [is] near [the] day of Yahweh and like devastation from [the] Almighty it will come.
16 Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
¿ Not before eyes our food has it been cut off from [the] house of God our joy and rejoicing.
17 Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
They have shriveled [the] seeds under shovels their they are desolate [the] storehouses they have been torn down [the] granaries for it has dried up [the] grain.
18 Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
How! it has groaned [the] livestock they have wandered in confusion [the] herds of cattle for not pasture [belongs] to them also [the] flocks of sheep they have suffered.
19 A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
To you O Yahweh I call for fire it has consumed [the] pastures of [the] wilderness and a flame it has set ablaze all [the] trees of the field.
20 Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.
Also [the] animals of [the] field it pants to you for they have dried up [the] channels of water and fire it has consumed [the] pastures of the wilderness.