< Yowel 3 >
1 “A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
“Ngalezonsuku langalesosikhathi, lapho sengibuyisela inotho kaJuda leJerusalema,
2 zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
ngizaqoqa izizwe zonke ngizehlisele eSigodini sikaJehoshafathi. Lapho-ke ngizazahlulela mayelana lelifa lami, abantu bami u-Israyeli ngoba zahlakazela abantu bami phakathi kwezizwe, zabelana ilizwe lami.
3 Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
Zenza inkatho ngabantu bami, zathenga izifebe ngabafana; zathengisa amankazana ngewayini ukuze zinathe.
4 “Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
Manje-ke lisolani ngami, wena Thire loSidoni lani lonke zifunda zaseFilistiya? Liyangiphindisela ngolutho engilwenzileyo na? Nxa lingiphindisela, ngizaphanga ngibuyisele elakwenzayo phezu kwamakhanda enu ngokuphangisa.
5 Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
Ngoba lathatha isiliva sami legolide lami lathwalela lenotho yami eligugu emathempelini enu.
6 Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
Lathengisa abantu bakoJuda laseJerusalema kumaGrikhi, ukuze libase khatshana lelizwe labo.
7 “Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
Khangelani, ngizabavusa ezindaweni elabathengisa kuzo, njalo ngizabuyisela phezu kwamakhanda enu lokho elakwenzayo.
8 Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
Ngizathengisa amadodana enu lamadodakazi enu ebantwini bakoJuda, njalo labo bazawathengisa kumaSabhini, isizwe esikhatshana.” UThixo usekhulumile.
9 Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
Memezelani lokhu ezizweni lithi: Lungiselani impi! Vusani amabutho! Wonke amadoda empi kasondele ahlasele.
10 Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
Khandani amakhuba enu abe zinkemba lemihedla yenu yokuthena izihlahla ibe yimikhonto. Obuthakathaka kathi, “Ngiqinile!”
11 Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
Wozani ngokuphangisa, lonke lina zizwe zasezinhlangothini zonke, libuthane khonapho. Yehlisa amabutho akho, Oh Thixo!
12 “Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
“Izizwe kazivuswe; kaziye eSigodini sikaJehoshafathi ngoba ngizahlala khona ukwehlulela izizwe zonke zasezinhlangothini zonke.
13 Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
Hehethani ngesikela ngoba okuvunwayo sekuvuthiwe. Wozani, gxobani amavini, ngoba isikhamelo sewayini sesigcwele lezimbizakazi seziphuphuma, bukhulu kangaka ububi bazo!
14 Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
Amaxuku, amaxuku esigodini sesinqumo! Ngoba usuku lukaThixo luseduze esigodini sezinqumo.
15 Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
Ilanga lenyanga kuzakuba mnyama, lezinkanyezi zingabe zisakhanya.
16 Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
UThixo uzavungama eseZiyoni aphinde akhwaze eseJerusalema; umhlaba lomkhathi kuzagedezela. Kodwa uThixo uzakuba yisiphephelo sabantu bakhe, inqaba yabantu bako-Israyeli.”
17 “Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
“Ngakho lizakwazi ukuthi mina, uThixo uNkulunkulu wenu, ngihlala eZiyoni, intaba yami engcwele. IJerusalema izakuba ngcwele; kayiyikuphinda ihlaselwe ngabezizweni futhi.
18 “A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
Ngalolosuku izintaba zizagobhoza iwayini elitsha, lamaqaqa ageleze uchago; zonke indonga zakoJuda zizageleza amanzi. Umthombo uzantuntuza endlini kaThixo uthambise isigodi saseShithima.
19 Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
Kodwa iGibhithe izachithakala, i-Edomi ibe yinkangala elugwadule, ngenxa yodlakela olwenziwa ebantwini bakoJuda lapho bachitha khona igazi elingelacala elizweni labo.
20 Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
KoJuda kuzahlalwa khona kuze kube nininini laseJerusalema kuzahlala izizukulwane zonke.
21 Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”
Umlandu wabo wegazi, engingakaxoli ngawo, ngizabaxolela ngawo.”