< Yowel 3 >

1 “A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
Jo redzi, tanīs dienās un tanī laikā, kad Es Jūda un Jeruzālemes cietumu atgriezīšu,
2 zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
Tad Es sapulcināšu visus pagānus un tos novedīšu uz Jehošafata ieleju un tur ar tiem tiesāšos Savu ļaužu dēļ un Sava īpašuma, Israēla, dēļ, ko tie izkaisījuši tautu starpā un izdalījuši Manu zemi.
3 Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
Un par Maniem ļaudīm tie meslus metuši un puisēnu devuši par mauku un meiteni pārdevuši par vīnu un ir dzēruši.
4 “Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
Un jūs no Tirus un Sidonas un visām Fīlistu robežām, kas jums ar Mani? Vai jūs Man ko gribat atdarīt, ko Es jums darījis, jeb vai jūs Man ko gribat padarīt? Ātri un piepeši Es to atmaksāšu uz jūsu galvu.
5 Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
Tāpēc ka jūs esat laupījuši Manu sudrabu un Manu zeltu, un Manus dārgumus nesuši savu dievekļu namos;
6 Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
Un Jūda bērnus un Jeruzālemes bērnus jūs esat pārdevuši Grieķiem, tos tālu aizdzīt no viņa robežām:
7 “Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
Redzi, Es tos uzmodināšu no tās vietas, kurp jūs tos esat pārdevuši, un atmaksāšu jūsu maksu uz jūsu galvām.
8 Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
Un Es jūsu dēlus un jūsu meitas pārdošu Jūdu bērniem rokā; tie tos pārdos uz Sabu, tautai, kas tālu dzīvo, - jo Tas Kungs to ir runājis.
9 Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
Izsauciet to starp pagāniem, svētījiet karu, pamodinājiet tos varenos, lai atnāk un ceļas visi karavīri.
10 Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
Kaļat savus lemešus par zobeniem un savas cirpes par šķēpiem! Vājais lai saka: es esmu stiprs!
11 Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
Sapulcējaties un nāciet šurp, visas tautas visapkārt, un sakrājaties! Turp noved, Kungs, savus varenos!
12 “Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
Tautas lai ceļas un sanāk Jehošafata ielejā, jo tur Es sēdēšu un tiesāšu visas tautas visapkārt.
13 Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
Pieliekat cirpi, jo pļaujamais ir gatavs; nāciet, minat, jo vīna spaids ir pilns, un trauki tek pāri, jo viņu blēdība ir liela.
14 Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
Troksnis, troksnis tai tiesas ielejā, jo Tā Kunga diena ir tuvu klāt tiesas ielejā.
15 Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
Saule un mēnesis aptumšojās un zvaigznes ierauj savu spožumu.
16 Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
Un Tas Kungs rūc no Ciānas, un no Jeruzālemes viņš paceļ Savu balsi, tā ka debess un zeme dreb. Bet Tas Kungs ir patvērums Saviem ļaudīm un stiprums Israēla bērniem.
17 “Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
Un jūs manīsiet, ka Es esmu Tas Kungs, jūsu Dievs, kas dzīvo Ciānā, Savā svētā kalnā, un Jeruzāleme būs svēta vieta, un sveši tur vairs neies cauri.
18 “A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
Un tai dienā pilēs salds vīns no kalniem un piens tecēs no pakalniem, un visi Jūda strauti būs pilni ūdens, un avots izlēks no Tā Kunga nama, tas slacinās visu Sitimas ieleju.
19 Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
Ēģipte taps postā un Edoms par tukšu vietu, tā varas darba dēļ, kas darīts pie Jūda bērniem, kuru zemē tie izlējuši nenoziedzīgas asinis.
20 Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
Bet Jūda pastāvēs mūžīgi un Jeruzāleme uz cilšu ciltīm.
21 Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”
Un Es atriebšu tās asinis, ko Es vēl nebiju atriebis. Un Tas Kungs dzīvos Ciānā.

< Yowel 3 >