< Yowel 3 >

1 “A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
For lo! in those days, and at that time, —when I shall bring back the captivity of Judah and Jerusalem,
2 zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
Then will I gather all the nations, and bring them down into the Vale of Jehoshaphat, —and will enter into judgment with them there, concerning my people, and mine inheritance Israel, whom they scattered among the nations, and, my land, they apportioned;
3 Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
And, for my people, they cast lots, —and gave a boy for a harlot, and a girl sold they for wine—and drank.
4 “Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
Moreover also, what have, ye, to do with me, O Tyre and Zidon, and all the circuit of Palestine? A recompense, are ye paying back unto me? But, though ye should make a recompense unto me, swiftly, speedily, would I return your recompense upon your own head.
5 Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
Because, my silver and my gold, ye took away, —and, my richly beautiful things, carried ye into your temples;
6 Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
And, the sons of Judah and the sons of Jerusalem, ye sold to the sons of Greece, —that they might be far removed from their own boundary.
7 “Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
Behold me! rousing them up out of the place whither ye sold them, —So will I bring back your dealing upon your own head.
8 Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
And I will sell your sons and your daughters into the hand of the sons of Judah, and they will sell them to Sabeans, unto a nation afar off, —for, Yahweh, hath spoken.
9 Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
Proclaim ye this, among the nations, Hallow a war, rouse the mighty ones, let them draw near, come up, all the men of war!
10 Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
Beat your plough-shares into swords, and your pruning-hooks into spears, —as for the weak, let him say, mighty, I am.
11 Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
Give help—and come in, all ye nations on every side, and gather yourselves together, —Thither, bring down, O Yahweh, thy mighty ones!
12 “Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
Let the nations, be roused, and come up, into the Vale of Jehoshaphat, —for, there, will I sit to judge all the nations, on every side.
13 Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
Thrust ye in the vintage knife, for, grown ripe, is the vintage, —Go in, tread down, for full is the winepress, flow over do the vats, for abundant is their wickedness.
14 Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
Multitudes, multitudes, in the vale of strict decision, —for near is the day of Yahweh, in the vale of strict decision.
15 Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
The sun and the moon, have become dark, —and, the stars, have withdrawn their shining,
16 Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
And, Yahweh, out of Zion, will roar, and, out of Jerusalem, will utter his voice, and the heavens and the earth, shall tremble, —but, Yahweh, shall be a shelter to his people, and a refuge to the sons of Israel.
17 “Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
So shall ye know that, I, Yahweh, am your God, making my habitation in Zion my holy mountain, —So shall, Jerusalem, be, holy, and, foreigners, shall pass through her no more.
18 “A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
And it shall come to pass in that day, that the mountains shall drip sweet wine, and the hills shall flow down with milk, and, all the channels of Judah, shall flow down with waters, —and, a spring, out of the house of Yahweh, shall come forth, and shall water the torrent-valley of the acacias.
19 Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
Egypt, to a desolation, shall be turned, and, Edom, to a desert most desolate, shall be changed, —because of the violence done to the sons of Judah, in that they shed innocent blood in their land.
20 Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
But, Judah, age-abidingly, shall remain, and, Jerusalem, to generation after generation.
21 Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”
And I will free from their blood-guiltiness them whom I had not freed, —for, Yahweh, is about to make his habitation in Zion.

< Yowel 3 >