< Yowel 3 >
1 “A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
For, in those days and in that time, when I bring back again the captivity of Judah and Jerusalem,
2 zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
I will also gather all the nations and bring them down into the Valley of Jehoshaphat, and there I will enter into judgment with them for my people and my heritage Israel, whom they have scattered among the nations, and divided my land.
3 Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
They have cast lots for my people. They have traded boys for prostitutes, and sold girls for wine, and drunk it.
4 “Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
What are you to me, Tyre and Sidon and all the districts of Philistia? Were you repaying any deed of mine, or were you doing something for me? Quickly will I return your deed upon your heads.
5 Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
You who have taken my silver and my gold, and you have brought my goodly jewels into your palaces,
6 Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
you have sold the people of Judah and of Jerusalem to the Greeks, so that you might remove them far from their own borders.
7 “Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
I am about to stir them up from the place to which you have sold them, and I will turn your deeds upon your own head.
8 Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
I will sell your sons and your daughters into the hands of the people of Judah, and they will sell them to the Sabeans, to a nation far off, for the Lord has spoken.
9 Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
Proclaim this among the nations, sanctify war. Arouse the warriors, let all the fighting men muster and go up.
10 Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
Beat your ploughshares into swords, and your pruning-hooks into lances; let the weak say, I, indeed, am strong.
11 Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
Bestir yourselves and come, all you nations round about. Quickly gather yourselves together, ask the Lord to bring his warriors.
12 “Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
Let the nations rouse themselves and come up to the Valley of Jehoshaphat, for there will I sit to judge all the surrounding nations.
13 Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
Put in the sickle, for the harvest is ripe; go in, tread, for the wine press is full. The vats overflow, for great is their wickedness.
14 Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
Noisy multitudes, noisy multitudes in the valley of decision. For near is the Lord’s day in the valley of decision!
15 Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
Sun and moon have turned dark, and the stars withdrawn their shining.
16 Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
Whenever the Lord roars from Zion and utters his voice from Jerusalem, earth and sky quake; but the Lord is a refuge to his people, and a fortress to the people of Israel.
17 “Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
And you will know that I am the Lord your God, I who dwells in Zion, my holy mountain, and Jerusalem will be holy, and strangers will not pass through her any more.
18 “A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
In that day, the mountains will drop sweet wine, the hills will flow with milk, all the channels of Judah will flow with water, a fountain will spring from the house of Judah, and will water the Valley of Shittim.
19 Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
Egypt will become a desolation, and Edom a wilderness, because of the violence done to the people of Judah, because they shed innocent blood in their land,
20 Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
Judah will remain inhabited forever, and Jerusalem from generation to generation.
21 Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”
I will avenge their blood which I have not yet avenged. The Lord lives in Zion!