< Yowel 3 >
1 “A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
For behold, in those days and at that time, When I shall bring back the captives of Judah and Jerusalem,
2 zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
I will assemble all the nations, And will bring them down it to the valley of Jehoshaphat, And there will I contend with them for my people and inheritance, Israel; Because they scattered them among the nations, And divided my land among themselves.
3 Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
Yea, they cast lots for my people, And gave a boy for a harlot, And sold a damsel for wine to drink.
4 “Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
What have ye to do with me, O Tyre and Sidon, And all the borders of Philistia? Will ye retaliate on me? Or will ye do anything against me? Swiftly and speedily will I bring back your doings upon your own head.
5 Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
Ye have taken my silver and my gold, And have carried into your palaces my precious, goodly things;
6 Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
The sons also of Judah, and the sons of Jerusalem, Ye have sold to the Grecians, That ye might remove them far from their border.
7 “Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
Behold, I will raise them out of the place whither ye have sold them, And I will return your injury upon your own head;
8 Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
I will sell your sons and your daughters into the hand of the sons of Judah, And they shall sell them to the Sabeans, to a nation afar off; For Jehovah hath spoken it.
9 Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
Proclaim ye this among the nations: “Prepare war! Stir up the mighty ones! Let all the warriors draw near; let them come up!”
10 Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
Beat your ploughshares into swords, And your pruning-hooks into spears; Let the weak say, I am strong!
11 Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
Assemble yourselves and come, all ye nations round about; Gather yourselves together! Thither, O Jehovah, bring down thy mighty ones!
12 “Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
Let the nations rise and come up to the valley of Jehoshaphat! For there will I sit to judge all the nations around.
13 Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
Put ye in the sickle, for the harvest is ripe; Come and tread, for the wine-press is full; The vats overflow; For their wickedness is great!
14 Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
The multitudes, the multitudes in the valley of judgment! For the day of Jehovah is near in the valley of judgment.
15 Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
The sun and the moon are darkened, And the stars withdraw their shining.
16 Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
Jehovah also will roar from Zion, And utter his voice from Jerusalem; The heavens and the earth shall shake. But Jehovah will be a refuge to his people! A strong-hold to the sons of Israel.
17 “Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
Then shall ye know that I am Jehovah your God, Dwelling in Zion, my holy mountain; And Jerusalem shall be holy; Strangers shall pass through her no more.
18 “A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
In that day shall the mountains drop down new wine, And the hills shall flow with milk. And all the streams of Judah shall flow with water. A fountain shall come forth from the house of Jehovah, That shall water the valley of Shittim.
19 Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
Egypt shall be a waste, And Edom a desolate wilderness, For their violence against the sons of Judah; For they shed innocent blood in their land.
20 Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
But Judah shall be inhabited for ever, And Jerusalem from generation to generation.
21 Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”
And I will avenge their blood, which I have not avenged, And Jehovah will dwell upon Zion.