< Yowel 3 >
1 “A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
At that time when this happens, when I bring back the exiles to Judah and Jerusalem,
2 zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
I will gather together all the nations in the valley of Jehoshaphat and I will judge them there over my people Israel, my inheritance, whom they have scattered among the nations, and have divided up my land.
3 Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
They cast lots for my people; they traded boys in payment for prostitutes and girls to buy wine to drink.
4 “Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
Also, what have you got to do with me, Tyre and Sidon, and all the regions of Philistia? Are you trying to get back at me? If you are trying to pay me back, I will quickly pay you back what you deserve for what you've done.
5 Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
You stole my silver and my gold and my best treasures, and you put them in your temples.
6 Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
You sold the people of Judah and Jerusalem to the Greeks so they could be sent far away from their land.
7 “Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
But watch out! I will get them moving from the places you sold them to, and bring them back, and I will pay you back what you deserve for what you've done.
8 Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
I will sell your sons and daughters to the people of Judah, and they will sell them to the Sabeans, a distant nation. I the Lord have spoken.
9 Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
Proclaim this among the nations: “Prepare for war! Call up the mighty warriors! Let all the soldiers get ready and advance!
10 Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
Hammer your plough blades and turn them into swords. Turn your pruning hooks into spears. Even the weak should say ‘I am a strong fighter!’
11 Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
Hurry up and come, all nations from everywhere, and gather there. Bring down your warriors, Lord!
12 “Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
Let the nations get ready, let them come to the valley of Jehoshaphat for there I will sit in judgment on all the nations.
13 Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
Start swinging the sickle, for the harvest is ripe. Come and tread the grapes for the winepress is full and the vats are overflowing because their wickedness has become so great.
14 Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
Huge mobs are in the valley of the Lord's verdict. For the day of the Lord is near in the valley of his verdict.
15 Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
The sun and moon will become dark, and the stars will stop shining.
16 Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
The Lord will roar from Zion, shouting in a loud voice from Jerusalem, shaking the heavens and the earth. But the Lord will shelter his people, protecting the people of Israel.
17 “Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
Then you will know that I, the Lord your God, dwell in Zion, my holy mountain, and Jerusalem will be a holy place forever, and no foreigners will ever march through her again.
18 “A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
At that time new wine will pour down the mountains, and the hills will flow with milk, and all the riverbeds of Judah will run with water. A spring will flow out of the Temple and will water the valley of Shittim.
19 Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
But Egypt will become desolate, and Edom a desert wasteland, because of the violence they did against Judah, for in their land they shed innocent blood.
20 Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
Judah will be lived in forever, and Jerusalem for all generations.
21 Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”
Will I pardon and leave unpunished the shedding of innocent blood? The Lord lives in Zion!”