< Yowel 3 >

1 “A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
Thi se, i de samme Dage og paa den samme Tid, naar jeg omvender Judas og Jerusalems Fangenskab,
2 zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
da vil jeg samle alle Hedningerne og føre dem ned til Josafats Dal; og der vil jeg gaa i Rette med dem om mit Folk og Israel min Arv; thi de have spredt dem iblandt Hedningerne og delt mit Land.
3 Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
Og de have kastet Lod om mit Folk og givet en ung Dreng for en Skøge og solgt en ung Pige for Vin, som de have drukket.
4 “Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
Men ogsaa, hvad ere I for mig, du Tyrus og Zidon, og I, alle Filisternes Lande? mon I ville gengælde mig for, hvad jeg har gjort, eller ville I gøre mig noget? snart, hastelig skal jeg lade Gengældelsen komme over eders Hoved;
5 Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
I, som have taget mit Sølv og mit Guld og bragt mine bedste Kostbarheder ind i eders Templer;
6 Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
og Judas Børn og Jerusalems Børn have I solgt til Grækernes Børn, for at føre dem langt bort fra deres Landemærke.
7 “Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
Se, jeg vækker dem op fra det Sted, hvorhen I solgte dem, og jeg vil lade Gengældelsen komme over eders Hoved.
8 Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
Og jeg vil sælge eders Sønner og eders Døtre i Judas Børns Haand, og de skulle sælge dem til Sabæerne, til et fjernt Folk; thi Herren har talt det.
9 Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
Udraaber dette iblandt Hedningerne, helliger en Krig, opvækker de vældige, lader alle Krigsmændene komme frem, drage op!
10 Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
Smeder eders Hakker om til Sværd og eders Vingaardsknive til Spyd; den svage sige: En Helt er jeg!
11 Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
Skynder eder og kommer, alle Hedninger, trindt omkring fra, og samler eder! did lade du, o Herre, dine vældige stige ned!
12 “Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
Opvækkes skulle Hedningerne og drage op til Josafats Dal; thi der vil jeg sidde, at dømme alle Hedningerne trindt omkring fra.
13 Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
Lægger Seglen til, thi Høsten er moden; kommer, stiger ned, thi Vinpersen er fuld, Persekarrene løbe over; thi stor er deres Ondskab.
14 Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
Skarer paa Skarer i Dommens Dal! thi nær er Herrens Dag i Dommens Dal.
15 Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
Sol og Maane sortne, og Stjerner forholde deres Skin.
16 Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
Og Herren skal brøle fra Zion og lade sin Røst lyde fra Jerusalem, og Himmel og Jord skulle ryste; men Herren skal være en Tilflugt for sit Folk og et Værn for Israels Børn.
17 “Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
Og I skulle fornemme, at jeg er Herren eders Gud, som bor paa Zion, mit hellige Bjerg; og Jerusalem skal vorde en Helligdom, og fremmede skulle ikke ydermere drage over den.
18 “A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
Og det skal ske paa denne Dag, at Bjergene skulle dryppe med Most, og Højene skulle flyde med Mælk, og alle Strømme i Juda skulle rinde med Vand, og der skal udgaa en Kilde fra Herrens Hus, og den skal vande Sittims Dal.
19 Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
Ægypten skal blive øde, og Edom skal blive til en øde Ørk, formedelst Voldsgerning imod Judas Børn, eftersom de have udøst uskyldigt Blod i deres Land.
20 Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
Men Juda skal blive evindelig og Jerusalem fra Slægt til Slægt.
21 Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”
Og jeg vil sone deres Blod, som jeg ikke havde sonet; og Herren bor paa Zion.

< Yowel 3 >