< Yowel 2 >

1 Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
Blow trumpets on Zion [Hill], God’s sacred hill [in Jerusalem]! Tell the people of Judah that they should tremble, because it will soon be the time for Yahweh [to punish us further].
2 rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
[That will be a very] dark and gloomy day; there will be [black] clouds and it will be very dark. A huge [swarm of locusts] has covered the mountains like [SIM] a black [cloud]. Nothing like this has ever happened before, and nothing like this will ever [happen] again.
3 A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
[It is as though the locusts bring] flames of fire from which no one can escape. In front of them, the land was [beautiful] like [SIM] the garden of Eden, but behind them [the land is like] a desert and nothing survives.
4 Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
[The locusts] resemble horses, and they run like [SIM] war horses.
5 Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
Leaping over the mountaintops, they make a noise like rumbling chariots, like [SIM] a mighty army that is preparing for a battle, or like [SIM] the roar of a fire that burns up stubble [in a field].
6 Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
When people see them coming, they become very pale and frightened.
7 Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
[The locusts] climb over walls like soldiers do; they march along in columns and never turn aside [from their columns].
8 Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
They rush straight ahead without pushing each other. [Even though people throw] spears and javelins at them, that will not cause them to stop.
9 Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
They swarm over the city walls and enter our houses; they enter through our windows like [SIM] thieves do.
10 A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
[It is as though] they cause the earth to shake and the sky to tremble. The sun and the moon become dark and the stars do not shine [because there are so many locusts in the sky].
11 Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
Yahweh leads this army [of countless locusts], and they obey his commands. This time when he is judging and punishing us is very terrible, [with the result that it seems that] no one [RHQ] can survive it.
12 “Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
But Yahweh says, “In spite of [these disasters that you have experienced], you can return to me with all your inner beings. Weep, and mourn, and (fast/abstain from eating food) [to show that you are sorry for having abandoned me].
13 Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
Do not tear your clothes [to show that you are sorry]; instead, show [MET] that you are sorry.” Yahweh is merciful and kind; he does not quickly become angry; he faithfully loves [people]. He does not quickly become angry; instead, he greatly and faithfully loves [you], and he does not like to punish you.
14 Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
No one knows [RHQ] if he will change his mind [about punishing you] and if instead he will act mercifully [toward you]. If he does that, he will bless you [by giving you plenty of grain and wine] in order that you can offer [some of] those things as sacrifices to him.
15 A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
Blow the trumpets on Zion [Hill]! Gather the people together! Show by fasting that you are sorry [for the sins that you have committed].
16 A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
Perform the rituals to cause yourselves to be acceptable to Yahweh. Gather everyone together— the old people and the children, even the babies, and summon brides and bridegrooms from their rooms.
17 Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
Tell the priests who serve Yahweh to cry between the altar and the entrance to the temple and to pray [this]: “Yahweh, rescue/save [us] your people; do not allow people from other nations to despise us; do not allow them to ridicule us and say, ‘Why has [RHQ] their God [abandoned them]?’”
18 Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
But Yahweh [showed that he] was concerned about his people and that he would act mercifully toward them.
19 Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
When the people prayed, Yahweh answered and said, “I will give you [plenty of] grain and wine and [olive] oil, and you will be satisfied. And I will no longer allow other nations to insult you.
20 “Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
Another army [of locusts will come] from the north [to attack you], but I will force them to continue [past Jerusalem] into the desert. Some will go into the Dead Sea in the east and some will go into the [Mediterranean] Sea in the west. [There] they will [all die, and their bodies] will stink.” Yahweh does great things!
21 Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
He does wonderful things! So even the ground should rejoice!
22 Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
And the wild animals should not be afraid, because the meadows will soon become green again; the fig trees and [other] trees will be full of fruit, and the grapevines will be covered with grapes.
23 Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
You people of Jerusalem, rejoice about what Yahweh, your God, [will be doing for you]. He will send abundant rain at the (right time/time when it is needed)— (in the spring/early in the year) and (in the autumn/late in the year) like he did previously.
24 Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
The ground where you thresh the grain will be covered with grain, and your vats where you store grape juice and [olive] oil will be full.
25 “Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
[Yahweh said, ] “I will repay you for everything that was destroyed by those great swarms of locusts that I sent to attack you.
26 Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
You, my people, will eat until your stomachs are full. Then you will praise me [MTY], Yahweh, your God, for the wonderful things that I have done for you. And never again will you be disgraced.
27 Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
When that happens, you will know that I am [always] among you, and that I am Yahweh, your God, and that there is no other [God]. Never again will you be disgraced.”
28 “Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
“Some time later, I will give my Spirit to many [HYP] people. Your sons and daughters will proclaim messages that come directly from me. Your old men will have dreams [that come from me], and your young men will have visions [that come from me].
29 Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
At that time, I will give my Spirit even to servants, both men and women.
30 Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
I will do unusual/amazing things on the earth and in the sky. [On the earth] [CHI], there will be much blood [shed] and [there will be very large] fires and smoke that resembles huge clouds.
31 Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
[In the sky, ] the sun will become dark and the moon will become [as red as] [MET] blood. [Those things will happen] before that great and terrible day when [I], Yahweh, appear.
32 Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.
But at that time [I] will save everyone who worships me. I promise that some people in Jerusalem [DOU] will escape [those disasters]; those whom I have chosen will survive.”

< Yowel 2 >