< Yowel 2 >

1 Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
Give a blast on a ram's horn in Zion and sound a battle signal on [the] mountain of holiness my let them tremble all [the] inhabitants of the land for [is] about to come [the] day of Yahweh for [it is] near.
2 rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
A day of darkness and gloom a day of cloud and thick darkness like dawn spread out over the mountains a people numerous and mighty like it not it has occurred since antiquity and after it not it will repeat until years of a generation and a generation.
3 A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
Before it it has consumed fire and after it it sets ablaze a flame [is] like [the] garden of Eden the land before it and after it a wilderness of desolation and also escape not it belongs to it.
4 Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
[is] like [the] appearance of Horses appearance its and like horsemen so they run!
5 Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
Like [the] sound of chariots over [the] tops of the mountains they leap! like [the] sound of a flame of fire consuming stubble like a people mighty deployed of battle.
6 Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
From before it they are in anguish peoples all faces they gather a glow.
7 Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
Like warriors they run! like men of war they go up a wall and each on ways its they go! and not they exchange! paths their.
8 Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
And each brother its not they crowd! a man on track its they go! and through the weapon[s] they fall not they stop.
9 Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
On the city they rush on the wall they run! in the houses they go up through the windows they go like thief.
10 A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
Before it it trembles [the] earth they shake [the] heavens sun and moon they become dark and [the] stars they withdraw brightness their.
11 Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
And Yahweh he gives forth voice his before army his for [is] great very camp his for [is] mighty [the] [one who] does word his for [is] great [the] day of Yahweh and awesome exceedingly and who? will he endure it.
12 “Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
And also now [the] utterance of Yahweh return to me with all heart your and with fasting and with weeping and with wailing.
13 Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
And tear heart your and may not [it be] garments your and return to Yahweh God your for [is] gracious and compassionate he long of anger and great of covenant loyalty and relenting on harm.
14 Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
Who? [is] knowing he will turn and he will relent and he will leave behind him a blessing a grain offering and a drink offering for Yahweh God your.
15 A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
Give a blast on a ram's horn in Zion consecrate a fast call an assembly.
16 A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
Gather [the] people consecrate an assembly gather [the] elders gather children and suckling-children of breasts let him go out [the] bridegroom from room his and [the] bride from chamber her.
17 Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
Between the porch and to the altar let them weep the priests [the] servants of Yahweh and let them say have compassion! O Yahweh on people your and may not you make inheritance your into a reproach to mock on them nations why? will people say among the peoples where? [is] God their.
18 Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
And he became jealous Yahweh for land his and he had compassion on people his.
19 Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
And he answered Yahweh and he said to people his here I [am] about to send to you grain and new wine and fresh oil and you will be satisfied with it and not I will make you again a reproach among the nations.
20 “Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
And the northerner[s] I will remove far away from with you and I will drive away it into a land dry and desolation face its into the sea eastern and end its into the sea western and it will go up stench its and it will go up foul smell its for he has made great to do.
21 Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
May not you fear O land be glad and rejoice for he has made great Yahweh to do.
22 Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
May not you fear O animals of [the] field for they are green [the] pastures of [the] wilderness for [the] tree[s] it has borne fruit its [the] fig tree and [the] vine they have given strength their.
23 Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
And O people of Zion be glad and rejoice in Yahweh God your for he has given to you the early rain for righteousness and he has sent down for you rain early rain and spring rain in the first [month].
24 Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
And they will be full the threshing floors grain and they will overflow the wine-vats new wine and fresh oil.
25 “Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
And I will restore to you the years which it has eaten the locust[s] the locust[s] and the locust[s] and the locust[s] army my great which I sent among you.
26 Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
And you will eat completely and being satisfied and you will praise [the] name of Yahweh God your who he has dealt with you by doing wonderfully and not they will be ashamed people my for ever.
27 Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
And you will know that [am] in [the] midst of Israel I and I [am] Yahweh God your and there not [is] yet and not they will be ashamed people my for ever.
28 “Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
And it will be after thus I will pour out spirit my on all flesh and they will prophesy sons your and daughters your old [men] your dreams they will dream! young men your visions they will see.
29 Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
And also on the [male] servants and on the female servants in the days those I will pour out spirit my.
30 Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
And I will put wonders in the heavens and on the earth blood and fire and columns of smoke.
31 Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
The sun it will be changed into darkness and the moon into blood before comes [the] day of Yahweh great and awesome.
32 Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.
And it will be every [one] who he will call on [the] name of Yahweh he will escape for on [the] mountain of Zion and in Jerusalem it will be an escaped remnant just as he has said Yahweh and among the survivors whom Yahweh [will be] calling.

< Yowel 2 >