< Yowel 2 >
1 Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
Blow ye the trumpet in Zion, and sound an alarm in my holy mountain. Let all the inhabitants of the land tremble. For the day of Jehovah comes, for it is near at hand,
2 rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
a day of darkness and gloominess, a day of clouds and thick darkness, as the dawn spreads upon the mountains, a great people and a strong, there has not ever been the like, nor shall be any more after them, even to the years of many generations.
3 A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
A fire devours before them, and behind them a flame burns. The land is as the garden of Eden before them, and behind them a desolate wilderness. Yea, and none has escaped them.
4 Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
The appearance of them is as the appearance of horses, and as horsemen, so do they run.
5 Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
They leap like the noise of chariots on the tops of the mountains, like the noise of a flame of fire that devours the stubble, as a strong people set in battle array.
6 Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
At their presence the peoples are in anguish; all faces have grown pale.
7 Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
They run like mighty men. They climb the wall like men of war, and they march each one on his ways. And they do not break their ranks.
8 Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
Neither does one push another. They march each one in his path, and they burst through the weapons, and do not break off.
9 Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
They leap upon the city. They run upon the wall. They climb up into the houses. They enter in at the windows like a thief.
10 A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
The earth quakes before them. The heavens tremble. The sun and the moon are darkened, and the stars withdraw their shining.
11 Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
And Jehovah utters his voice before his army, for his camp is very great. For he is strong who executes his word. For the day of Jehovah is great and very fearful, and who can abide it?
12 “Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
Yet even now, says Jehovah, turn ye to me with all your heart, and with fasting, and with weeping, and with mourning.
13 Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
And rend your heart, and not your garments, and turn to Jehovah your God, for he is gracious and merciful, slow to anger, and abundant in loving kindness, and relents of the evil.
14 Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
Who knows whether he will not turn and relent, and leave a blessing behind him, even a meal offering and a drink offering to Jehovah your God?
15 A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
Blow the trumpet in Zion. Sanctify a fast. Call a solemn assembly.
16 A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
Gather the people. Sanctify the assembly. Assemble the old men. Gather the sons, and those who suck the breasts. Let the bridegroom go forth from his chamber, and the bride out of her closet.
17 Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
Let the priests, the ministers of Jehovah, weep between the porch and the altar, and let them say, Spare thy people, O Jehovah, and do not give thy heritage to reproach, that the nations should rule over them. Why should they say among the peoples, Where is their God?
18 Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
Then Jehovah was jealous for his land, and had pity on his people.
19 Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
And Jehovah answered and said to his people, Behold, I will send you grain, and new wine, and oil, and ye shall be satisfied therewith. And I will no more make you a reproach among the nations.
20 “Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
But I will remove the northern army far off from you, and will drive it into a land barren and desolate, its forepart into the eastern sea, and its rear part into the western sea. And its stench shall come up, and its foul odor shall come up, because it has done great things.
21 Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
Fear not, O land. Be glad and rejoice, for Jehovah has done great things.
22 Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
Be not afraid, ye beasts of the field, for the pastures of the wilderness spring, for the tree bears its fruit, the fig tree and the vine yield their strength.
23 Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
Be glad then, ye sons of Zion, and rejoice in Jehovah your God, for he gives you the former rain in just measure, and he causes the rain to come down for you, the former rain and the latter rain, in the first month.
24 Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
And the floors shall be full of wheat, and the vats shall overflow with new wine and oil.
25 “Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
And I will restore to you the years that the locust, the canker-worm, and the caterpillar, and the palmer-worm has eaten-my great army which I sent among you.
26 Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
And ye shall eat in plenty and be satisfied. And shall praise the name of Jehovah your God, who has dealt wondrously with you. And my people shall never be put to shame.
27 Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
And ye shall know that I am in the midst of Israel, and that I am Jehovah your God, and there is none else. And my people shall never be put to shame.
28 “Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
And it shall come to pass afterward, that I will pour out my Spirit upon all flesh, and your sons and your daughters shall prophesy. Your old men shall dream dreams. Your young men shall see visions.
29 Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
And also I will pour out my Spirit upon the servants and upon the handmaids in those days.
30 Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
And I will show wonders in the heavens and in the earth, blood, and fire, and pillars of smoke.
31 Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
The sun shall be turned into darkness, and the moon into blood, before the great and wonderful day of Jehovah comes.
32 Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.
And it shall come to pass, that whoever shall call on the name of Jehovah shall be saved. For in mount Zion and in Jerusalem there shall be those who escape, as Jehovah has said, and among the remnant those whom Jehovah calls.