< Yowel 1 >

1 Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
Ilizwi leNkosi elafika kuJoweli indodana kaPethuweli.
2 Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
Zwanini lokhu, badala, libeke indlebe, lonke bahlali belizwe. Kwake kwenzeka lokhu yini ensukwini zenu, kumbe lensukwini zaboyihlo?
3 Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
Landiselani abantwana benu ngakho, labantwana benu abantwana babo, labantwana babo esinye isizukulwana.
4 Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
Okutshiywe zintothoviyane isikhonyane sikudlile; lokutshiywe yisikhonyane iqhwagi likudlile; lokutshiywe liqhwagi inswabanda ikudlile.
5 Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
Phaphamani, zidakwa, likhale inyembezi, liqhinqe isililo, lonke banathi bewayini, ngenxa yewayini elitsha, ngoba liqunyiwe lasuka emlonyeni wenu.
6 Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
Ngoba isizwe senyukele elizweni lami, esilamandla, esingelanani; amazinyo aso angamazinyo esilwane, silamazinyo emihlathi esilwane esisikazi.
7 Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
Senze ivini lami laba yincithakalo, lesihlahla sami somkhiwa saba zimvava; sakwebula lokukwebula, sakuphosela phansi, ingatsha zakho zaba mhlophe.
8 Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
Qhinqani isililo njengentombi emsulwa ebhinciswe isaka ngenxa yomyeni wobutsha bayo.
9 Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
Umnikelo wokudla lomnikelo wokunathwayo uqunyiwe wasuka endlini yeNkosi. Abapristi, izikhonzi zeNkosi, bayalila.
10 Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
Insimu ichithiwe, umhlabathi uyalila; ngoba amabele achithiwe, iwayini elitsha lomile, amafutha aphela amandla.
11 Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
Banini lenhloni, balimi, qhinqani isililo, baphathizivini, ngenxa yengqoloyi langenxa yebhali; ngoba isivuno sensimu sichithekile.
12 Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
Ivini libunile, lomkhiwa uphele amandla; ipomegranati, lesihlahla selala, lesihlahla se-aphula, zonke izihlahla zeganga zomile, ngoba intokozo ibunile yasuka ebantwaneni babantu.
13 Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
Bhincani, lilile, bapristi, qhinqani isililo, zikhonzi zelathi. Wozani, lilale ebusuku emasakeni, zikhonzi zikaNkulunkulu wami; ngoba umnikelo wokudla lomnikelo wokunathwayo kugodliwe endlini kaNkulunkulu wenu.
14 Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
Yehlukanisani ukuzila ukudla, libize umhlangano onzulu, libuthanise abadala, labo bonke abahlali belizwe, endlini yeNkosi uNkulunkulu wenu, likhale eNkosini.
15 Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
Maye ngalolosuku! Ngoba usuku lweNkosi luseduze, luzafika njengencithakalo evela kuSomandla.
16 Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
Ukudla kakuqunywanga yini phambi kwamehlo ethu, ukuthaba lentokozo kusuka endlini kaNkulunkulu wethu?
17 Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
Inhlanyelo iyabola ngaphansi kwamagade ayo; izibuya zingamanxiwa, iziphala zidilizelwe phansi, ngoba amabele abunile.
18 Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
Yeka ukububula kwezifuyo! Imihlambi yenkomo ididekile, ngoba kayilalo idlelo; lemihlambi yezimvu iyahlupheka.
19 A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
Ngiyakhala kuwe, Nkosi, ngoba umlilo uqedile amadlelo enkangala, lelangabi lilumathise zonke izihlahla zeganga.
20 Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.
Lenyamazana zeganga ziyakhala kuwe, ngoba izifudlana zamanzi zitshile, lomlilo uqede amadlelo enkangala.

< Yowel 1 >