< Yowel 1 >
1 Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
La parole de l’Éternel, qui vint à Joël, fils de Pethuel.
2 Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
Écoutez ceci, vieillards, et prêtez l’oreille, vous, tous les habitants du pays! Ceci est-il arrivé de vos jours, ou même dans les jours de vos pères?
3 Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
Racontez-le à vos fils, et vos fils à leurs fils, et leurs fils à une autre génération:
4 Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
ce qu’a laissé la chenille, la sauterelle l’a mangé; et ce qu’a laissé la sauterelle, l’yélek l’a mangé, et ce qu’a laissé l’yélek, la locuste l’a mangé.
5 Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
Réveillez-vous, ivrognes, et pleurez; et hurlez, vous tous, buveurs de vin, à cause du moût, car il est retranché à vos bouches.
6 Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
Car une nation est montée sur mon pays, forte et innombrable. Ses dents sont les dents d’un lion, et elle a les grosses dents d’une lionne.
7 Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
Elle a réduit ma vigne en une désolation, mon figuier en un tas de bois; elle l’a écorcé entièrement, et l’a jeté par terre; ses rameaux ont blanchi.
8 Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
Gémis comme une vierge ceinte du sac, sur le mari de sa jeunesse!
9 Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
L’offrande et la libation sont retranchées de la maison de l’Éternel; les sacrificateurs, les serviteurs de l’Éternel, mènent deuil;
10 Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
les champs sont ravagés, la terre mène deuil; car le blé est ravagé, le vin nouveau est honteux, l’huile languit.
11 Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
Soyez honteux, laboureurs; hurlez, vignerons, – à cause du froment et de l’orge, car la moisson des champs a péri!
12 Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
La vigne est honteuse, et le figuier languit, – le grenadier, le palmier aussi, et le pommier; tous les arbres des champs sont desséchés; car la joie est tarie du milieu des fils des hommes.
13 Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
Ceignez-vous et lamentez-vous, sacrificateurs; hurlez, vous qui servez l’autel; venez, passez la nuit sous le sac, vous qui servez mon Dieu! car l’offrande et la libation sont ôtées à la maison de votre Dieu.
14 Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
Sanctifiez un jeûne, convoquez une assemblée solennelle; assemblez les anciens, tous les habitants du pays, à la maison de l’Éternel, votre Dieu, et criez à l’Éternel!
15 Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
Hélas, quel jour! car le jour de l’Éternel est proche, et il viendra comme une destruction du Tout-puissant.
16 Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
La nourriture n’est-elle pas retranchée de devant nos yeux, [et], de la maison de notre Dieu, la joie et l’allégresse?
17 Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
Les semences pourrissent sous leurs mottes; les greniers sont désolés; les granges sont renversées, car le blé est desséché.
18 Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
Comme le bétail gémit! Les troupeaux de gros bétail sont déconcertés, car il n’y a pas de pâturage pour eux; les troupeaux de menu bétail aussi sont en peine.
19 A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
À toi, Éternel, je crierai; car le feu a dévoré les pâturages du désert, et la flamme a brûlé tous les arbres des champs.
20 Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.
Les bêtes des champs aussi crient à toi, car les cours d’eau sont desséchés, et le feu a dévoré les pâturages du désert.