< Ayuba 1 >

1 A ƙasar Uz akwai wani mutum mai suna Ayuba. Mutum ne marar laifi kuma mai adalci; yana tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.
A man he was in [the] land of Uz [was] Job name his and he was - the man that blameless and upright and fearing God and turning aside from evil.
2 Yana da’ya’ya maza bakwai da’yan mata uku,
And they were born to him seven sons and three daughters.
3 yana da tumaki dubu bakwai, raƙuma dubu uku, shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, yana kuma da masu yi masa aiki da yawa. A ƙasar Gabas ba wani kamar sa.
And it was livestock his seven thousand sheep and three thousand camels and five hundred pair[s] of ox[en] and five hundred female donkeys and service much very and he was the man that great more than all [the] people of [the] east.
4 ’Ya’yansa maza sukan yi biki a gidajensu, wannan yă yi yă ba wancan, sai su kira’yan’uwansu mata ukun su ci, su sha tare.
And they went sons his and they made a feast [the] house of each one day his and they sent and they invited [the] three (sisters their *Q(k)*) to eat and to drink with them.
5 Bayan lokacin bikin ya wuce, sai Ayuba yă aika su zo don yă tsarkake su. Tun da sassafe zai miƙa hadaya ta ƙonawa domin kowannensu, don yana tunani cewa, “Mai yiwuwa’ya’yana sun yi wa Allah zunubi, ko sun la’anta shi a cikin zuciyarsu.” Haka Ayuba ya saba yi.
And it was that they had gone round [the] days of the feast and he sent Job and he sanctified them and he rose early in the morning and he offered up burnt offerings [the] number of all of them for he said Job perhaps they have sinned children my and they have blessed God in heart their thus he did Job all the days.
6 Wata rana mala’iku suka kawo kansu gaban Ubangiji, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.
And it was the day and they came [the] sons of God to present themselves on Yahweh and he came also the adversary in midst of them.
7 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
And he said Yahweh to the adversary from where? are you coming and he answered the adversary Yahweh and he said from roving about on the earth and from going about on it.
8 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.”
And he said Yahweh to the adversary ¿ have you set heart your on servant my Job for there not [is] like him on the earth a man blameless and upright fearing God and [who] turns aside from evil.
9 Sai Shaiɗan ya amsa ya ce, “Haka kawai Ayuba yake tsoron Allah?
And he answered the adversary Yahweh and he said ¿ in vain has he feared Job God.
10 Ba ka kāre shi da iyalinsa gaba ɗaya da duk mallakarsa ba? Ka Albarkaci ayyukan hannunsa yadda dabbobinsa duk sun cika ko’ina.
¿ Not (you *Q(K)*) have you put a hedge behind him and behind house his and behind all that [belongs] to him from round about [the] work of hands his you have blessed and livestock his it has spread out in the land.
11 Ka ɗan miƙa hannunka ka raba shi da duk abin da yake da shi, ba shakka zai la’anta ka kana ji, kana gani.”
And but stretch out please hand your and touch all that [belongs] to him if not on face your he will bless you.
12 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.” Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji.
And he said Yahweh to the adversary there! all that [belongs] to him [is] in hand your only against him may not you stretch out hand your and he went out the adversary from with [the] presence of Yahweh.
13 Wata rana lokacin da’ya’yan Ayuba suke cikin biki a gidan babban ɗansa,
And it was the day and sons his and daughters his [were] eating and drinking wine in [the] house of brother their the firstborn.
14 sai ɗan aika ya zo wurin Ayuba ya ce masa, “Shanu suna huɗa, jakuna kuma suna kiwo nan kusa,
And a messenger he came to Job and he said the ox[en] they were plowing and the female donkeys [were] grazing on hands their.
15 sai Sabenawa suka auka musu suka kwashe su suka tafi, suka karkashe masu yi maka aiki duka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
And it fell Sabean[s] and it took them and the servants they struck to [the] mouth of [the] sword and I have escaped! only I to alone me to tell to you.
16 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Wutar Allah ta sauko daga sama ta ƙona dukan tumaki da masu lura da su, wato, bayinka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
Still - this [one] [was] speaking and this [one] he came and he said [the] fire of God it fell from the heavens and it burned the sheep and the servants and it consumed them and I have escaped! only I to alone me to tell to you.
17 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa sun auka wa raƙumanka sun kwashe su duka, suka kuma karkashe masu yi maka aiki, ni kaɗai ne na tsira na zo in gaya maka!”
Still - this [one] [was] speaking and this [one] he came and he said [the] Chaldeans they formed - three companies and they made a raid on the camels and they took them and the servants they struck to [the] mouth of [the] sword and I have escaped! only I to alone me to tell to you.
18 Yana cikin magana, sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “’Ya’yanka maza da mata suna biki, suna ci suna sha a gidan babban ɗanka,
Until this [one] [was] speaking and this [one] he came and he said sons your and daughters your [were] eating and drinking wine in [the] house of brother their the firstborn.
19 sai wata iska mai ƙarfi daga hamada ta auka ta rushe gidan, gidan kuwa ya fāɗi a kan’ya’yanka ya kashe su, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
And there! a wind great it came - from [the] other side of the wilderness and it touched [the] four [the] corners of the house and it fell on the youths and they died and I have escaped! only I to alone me to tell to you.
20 Da jin haka sai Ayuba ya tashi ya yayyaga tufafin jikinsa, ya aske kansa. Ya fāɗi a ƙasa ya yi sujada
And he arose Job and he tore robe his and he shaved head his and he fell [the] earth towards and he bowed down.
21 ya ce, “Tsirara na fito daga cikin mahaifiyata, tsirara kuma zan koma. Ubangiji ya bayar, Ubangiji kuma ya karɓa; yabo ya tabbata ga Ubangiji.”
And he said naked (I came out *Q(k)*) from [the] womb of mother my and naked I will return there towards Yahweh he gave and Yahweh he has taken may it be [the] name of Yahweh blessed.
22 Cikin wannan duka Ayuba bai yi wa Allah zunubi ta wurin ba shi laifi ba.
In all this not he sinned Job and not he ascribe unseemliness to God.

< Ayuba 1 >