< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
А Йов відповів та й сказав:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Справді пізнав я, що так. Та як оправда́тись люди́ні земній перед Богом?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Якщо вона схоче на прю стати з Ним, — Він відповіді їй не дасть ні на о́дне із тисячі ска́ржень.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Він мудрого серця й могутньої сили; хто був проти Нього упертий — і ці́лим зостався?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Він го́ри зриває, й не знають вони, що в гніві Своїм Він їх переверну́в.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Він землю трясе́ з її місця, і стовпи́ її тру́сяться.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Він сонцеві скаже, — й не сходить воно, і Він запеча́тує зо́рі.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Розтягує небо Він Сам, і хо́дить по мо́рських висо́тах,
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Він Во́за створив, Оріо́на та Волосожа́ра, та зо́рі півде́нні.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Він чинить велике та недосліди́ме, предивне, якому немає числа!
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Ось Він надо мною прохо́дить, та я не побачу, і Він пере́йде, а я не пригля́нусь до Нього
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Ось Він схо́пить кого, — хто заве́рне Його, хто скаже Йому: що́ Ти робиш?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Бог гніву Свойого не спи́нить, під Ним гнуться Рага́вові помічники́, —
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
що ж тоді відпові́м я Йому́? Які я слова́ підберу́ проти Нього,
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
я, який коли б був справедли́вий, то не відповідав би, я, що благаю свойо́го Суддю?
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Коли б я взива́в, а Він мені відповідь дав, — не повірю, що вчув би мій голос,
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Він, що бурею може розте́рти мене та помно́жити рани мої безневи́нно.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Не дає Він мені й зве́сти духа мого, бо мене насича́є гірко́тою.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Коли ходить про силу, то Він Всемогутній, коли ж ходить про суд, — хто посві́дчить мені?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Якщо б справедливим я був, то осу́дять мене мої у́ста, якщо я безневи́нний, то вчинять мене винува́тим.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Я невинний, проте́ своєї душі я не знаю, і не ра́дий життям своїм я.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Це одне, а тому́ я кажу́: невинного як і лукавого Він вигубля́є.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Якщо нагло бич смерть заподі́ює, — Він з про́би невинних сміється.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
У ру́ку безбожного да́на земля, та Він лиця су́ддів її закриває. Як не Він, тоді хто?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
А дні мої стали швидкіші, як той скорохо́д, повтікали, не бачили доброго,
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
промину́ли, немов ті човни́ очере́тяні, мов орел, що несеться на здо́бич.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Якщо я скажу́: Хай забуду своє наріка́ння, хай зміню́ я обличчя своє й підбадьо́рюся,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
то боюся всіх сму́тків своїх, і я знаю, що Ти не очи́стиш мене.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Все одно буду я́ винува́тий, то на́що надармо я мучитися бу́ду?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Коли б я умився снігово́ю водою, і почи́стив би лу́гом долоні свої,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
то й тоді Ти до гро́бу опу́стиш мене, і учи́нить бридки́м мене о́діж моя.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Бо Він не люди́на, як я, й Йому відповіді я не дам, і не пі́демо ра́зом на суд,
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
поміж нами нема посере́дника, що поклав би на нас на обо́х свою руку.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Нехай забере Він від мене Свойого бича́, Його ж страх хай мене не жахає,
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
тоді буду казати, й не буду боятись Його, бо я не такий сам з собою!

< Ayuba 9 >