< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Job svarade och sade:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Ja, jag vet det fullväl, att så är, att en menniska icke kan bestå rättfärdig för Gud.
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Täckes honom träta med honom, så kan han icke svara honom ett emot tusende.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Han är vis och mägtig; hvem hafver det dock gått väl af, som sig hafver satt emot honom?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Han försätter bergen, förr än de det förnimma; hvilka han i sine vrede omkastar.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Han rörer jordena af sitt rum, så att hennes pelare bäfva.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Han talar till solena, så går hon intet upp, och han förseglar stjernorna.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Han allena utsträcker himmelen, och går på hafsens vägar.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Han gör Karlavagnen ( på himmelen ) och Orion; sjustjernorna, och de stjernor söderut.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Han gör mägtig ting, som man icke utransaka kan, och under, deruppå intet tal är.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Si, han går framom mig, förr än jag varder det varse; och han förvandlar sig, förr än jag det märker.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Si, om han går hasteliga bort, ho vill hemta honom igen? Ho vill säga till honom: Hvad gör du?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Han är Gud, hans vrede kan ingen stilla; under honom måste buga sig de stolta herrar.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Huru skulle jag då svara honom, och finna några ord emot honom?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Om jag än rätt hafver, så kan jag dock likväl intet svara honom; utan måste i rättenom bedjas före.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Och om jag än åkallade honom, och han hörde mig; så tror jag dock icke, att han hörer mina röst.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Ty han far öfver mig med storm, och gör mig såren mång utan sak.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Han låter icke min anda vederqvickas, utan gör mig full med bedröfvelse.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Vill man magt, så är han för mägtig; vill man rätten, ho vill vittna med mig?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Om jag säger att jag är rättfärdig, så fördömer han mig dock; är jag from, så för han mig dock till ondan.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Är jag än from, så tör min själ dock intet hålla sig dervid; jag begärer intet mer lefva.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Det är det som jag sagt hafver; han förgör både den goda, och den ogudaktiga.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
När han begynner till att slå, så dräper han straxt, och begabbar de oskyldigas frestelse.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
Men landet varder gifvet under dens ogudaktigas hand, att han undertrycker dess domare; är det icke så, huru skulle det annars vara.
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Mine dagar hafva varit snarare än en löpare; de hafva flytt, och hafva intet godt sett.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
De äro förgångne såsom stark skepp; såsom en örn flyger till maten.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
När jag tänker: Jag vill glömma bort min klagan; jag vill förvandla mitt ansigte, och vederqvicka mig;
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Så fruktar jag mig för all min sveda, vetandes, att du icke låter mig vara oskyldig.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Är jag nu ogudaktig, hvi hafver jag då sådana onyttiga vedermödo?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Om jag än tvådde mig i snö, och gjorde mina händer rena i källo;
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Så doppar du mig dock i träck, och min kläder varda mig illa ståndande.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Ty han är icke min like, dem jag svara kunde, att vi måtte både komma för rätten.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Det är ingen, som oss åtskiljer; som sätter sina hand emellan oss båda.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Han tage sitt ris ifrå mig, och låte sin förskräckelse komma ifrå mig;
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Att jag må tala, och icke mer torf frukta för honom; ty jag vet mig oskyldig.

< Ayuba 9 >