< Ayuba 9 >
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Ciertamente yo sé que es así. ¿Pero cómo puede un hombre justificarse ante ʼElohim?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Aunque uno quiera disputar con Él, no le podría responder una vez entre 1.000.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Él es sabio de corazón y poderoso en fortaleza. ¿Quién se endureció contra Él y salió ileso?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Arranca las montañas con su furor, y no saben quién las trastornó.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Sacude la tierra de su lugar y estremece sus columnas.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Él manda al sol, y no brilla. Coloca sello a las estrellas.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Él solo extendió el cielo, y camina sobre las olas del mar.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Él hizo la Osa, el Orión, las Pléyades y las secretas cámaras del sur.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Él hace cosas grandiosas, inescrutables, y maravillas incontables.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Ciertamente pasa junto a mí y no lo veo. Si pasa adelante de mí, no lo percibo.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Si Él arrebata, ¿quién lo resistirá? ¿Quién le dirá: Qué haces?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
ʼElohim no reprime su ira. Bajo Él se abaten los que ayudan a los soberbios.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
¡Cuánto menos yo puedo replicarle, al rebuscar palabras frente a Él!
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
A Él yo, aunque sea recto, no me atrevo a responder. Más bien imploro la clemencia de mi Juez.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Si lo invoco, y Él me responde, no podría creer que me oye.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Porque me quebranta con una tormenta y multiplica mis heridas sin causa.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
No me deja recuperar aliento, mas bien me llena de amarguras.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Si apelo a la fuerza, ¡ciertamente Él es poderoso! Y si acudo al juicio, ¿quién lo convocará?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Si me declaro justo, mi boca me condenará. Aunque sea intachable, Él me declarará perverso.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Soy intachable, sin embargo, no me conozco a mí mismo. Desprecio mi vida.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Todo es una misma cosa. Por tanto digo: Él destruye al intachable y al perverso.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Si el azote mata de repente, Él se burla de la desesperación del inocente.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
La tierra es entregada en manos de los perversos. Él cubre los semblantes de sus jueces. Si no es así, ¿entonces, quién?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Mis días son más veloces que un corredor. Huyeron. No vieron el bien.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Se deslizaron como botes de junco, como el águila que se lanza sobre su presa.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Si digo: Olvidaré mi queja, mudaré mi semblante y me alegraré,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
entonces me turban todos mis dolores. Sé que no me tendrás como inocente,
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
y que soy declarado perverso. ¿Para qué entonces me fatigo en vano?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Aunque me lave con agua de nieve, y limpie mis manos con lejía,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
aún me hundirás en el lodo, y mis ropas me repugnarán.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Porque Él no es hombre como yo para que le responda, y vayamos juntos a juicio.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
No hay un árbitro entre nosotros que coloque su mano entre los dos,
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
que quite su vara de sobre mí para que no me espante su terror.
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Entonces yo hablaría y no le temería. Pero yo mismo no estoy en esa condición.