< Ayuba 9 >
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Заиста, знам да је тако; јер како би могао човек бити прав пред Богом?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Ако би се хтео прети с Њим, не би Му могао одговорити од хиљаде на једну.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Мудар је срцем и јак снагом; ко се је опро Њему и био срећан?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Он премешта горе, да нико и не опази; превраћа их у гневу свом;
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Он креће земљу с места њеног да јој се ступови дрмају;
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Он кад запрети сунцу, не излази; Он запечаћава звезде;
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Он разапиње небо сам, и гази по валима морским;
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Он је начинио звезде кола и штапе и влашиће и друге југу у дну;
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Он чини ствари велике и неиспитиве и дивне, којима нема броја.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Гле, иде мимо мене, а ја не видим; прође, а ја га не опазим.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Гле, кад ухвати, ко ће Га нагнати да врати? Ко ће Му казати: Шта радиш?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Бог не устеже гнева свог, падају пода Њ охоли помоћници.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
А како би Му ја одговарао и бирао речи против Њега?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Да сам и прав, нећу Му се одговорити, ваља да се молим судији свом.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Да Га зовем и да ми се одзове, још не могу веровати да је чуо глас мој.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Јер ме је вихором сатро и задао ми много рана низашта.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Не да ми да одахнем, него ме сити горчинама.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Ако је на силу, гле, Он је најсилнији; ако на суд, ко ће ми сведочити?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Да се правдам, моја ће ме уста осудити; да сам добар, показаће да сам неваљао.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Ако сам добар, нећу знати за то; омрзао ми је живот мој.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Свеједно је; зато рекох: и доброг и безбожног Он потире.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Кад би још убио бич наједанпут! Али се смеје искушавању правих.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
Земља се даје у руке безбожнику; лице судија њених заклања; ако не Он, да ко?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Али дани моји бише бржи од гласника; побегоше, не видеше добра.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Прођоше као брзе лађе, као орао кад лети за храну.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Ако кажем: Заборавићу тужњаву своју, оставићу гнев свој и окрепићу се;
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Страх ме је од свих мука мојих, знам да ме нећеш оправдати.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Бићу крив; зашто бих се мучио узалуд?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Да се измијем водом снежницом, и да очистим сапуном руке своје,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Тада ћеш ме замочити у јаму да се гаде на ме моје хаљине.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Јер није човек као ја да Му одговарам, да идем с Њим на суд;
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Нити има међу нама кмета да би ставио руку своју међу нас двојицу.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Нека одмакне од мене прут свој, и страх Његов нека ме не страши;
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Тада ћу говорити, и нећу Га се бојати; јер овако не знам за себе.