< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Então Job respondeu,
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
“Verdadeiramente eu sei que é assim, mas como o homem pode estar apenas com Deus?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Se ele tiver o prazer de contender com ele, ele não pode responder-lhe uma vez em mil.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Deus é sábio de coração, e poderoso em força. Quem se endureceu contra ele e prosperou?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Ele remove as montanhas, e eles não sabem disso, quando ele os derruba em sua raiva.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Ele sacode a terra para fora de seu lugar. Seus pilares tremem.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Ele comanda o sol e ele não nasce, e sela as estrelas.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Somente ele estica os céus, e pisadas nas ondas do mar.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Ele faz o Urso, Orion, e as Plêiades, e os quartos do sul.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Ele faz grandes coisas para além de descobrir; sim, coisas maravilhosas sem número.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Eis que ele passa por mim, e eu não o vejo. Ele também passa adiante, mas eu não o percebo.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Eis que ele se arrebata. Quem pode atrapalhá-lo? Quem lhe perguntará: “O que você está fazendo?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
“Deus não vai retirar sua raiva. Os ajudantes de Rahab se abaixam sob ele.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Quanto menos eu lhe responderei, e escolher minhas palavras para discutir com ele?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Embora eu fosse justo, ainda não lhe responderia. Eu faria súplicas ao meu juiz.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Se eu tivesse ligado, e ele tivesse me respondido, no entanto, eu não acreditaria que ele escutou a minha voz.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Pois ele me quebra com uma tempestade, e multiplica minhas feridas sem causa.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Ele não me permitirá recuperar meu fôlego, mas me enche de amargura.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Se é uma questão de força, eis que ele é poderoso! Se de justiça, 'Quem', diz ele, 'me convocará'?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Embora eu seja justo, minha própria boca me condenará. Embora eu seja irrepreensível, isso me mostrará perverso.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Estou irrepreensível. Eu não me respeito. Eu desprezo minha vida.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
“É tudo a mesma coisa. Portanto, eu digo que ele destrói os irrepreensíveis e os perversos.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Se o flagelo matar de repente, ele vai zombar do julgamento dos inocentes.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
A terra é entregue na mão dos ímpios. Ele cobre os rostos de seus juízes. Se não é ele, então quem é ele?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
“Agora meus dias são mais rápidos que os de um corredor. Eles fogem. Eles não vêem nada de bom.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Eles faleceram como os navios rápidos, como a águia que se precipita sobre a presa.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Se eu disser: 'Vou esquecer minha reclamação', Vou deixar minha cara triste, e me alegrar”.
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Tenho medo de todas as minhas mágoas. Eu sei que você não me considerará inocente.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Estarei condenado. Por que então eu trabalho em vão?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Se eu me lavar com neve, e limpar minhas mãos com lixívia,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
ainda assim, você me mergulhará na vala. Minhas próprias roupas me abominarão.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Pois ele não é um homem, como eu sou, que eu deveria responder-lhe, que devemos nos reunir para julgar.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Não há árbitro entre nós, que poderia colocar sua mão sobre nós dois.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Deixe-o tirar sua vara de mim. Que seu terror não me faça ter medo;
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
então eu falaria, e não o temeria, pois não estou assim em mim mesmo.

< Ayuba 9 >