< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Mas Jó respondeu, dizendo:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Na verdade sei que é assim; mas como pode o ser humano ser justo diante de Deus?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Ainda se quisesse disputar com ele, não conseguiria lhe responder uma coisa sequer em mil.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Ele é sábio de coração, e poderoso em forças. Quem se endureceu contra ele, e teve paz?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Ele transporta as montanhas sem que o saibam; e as transtorna em seu furor.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Ele remove a terra de seu lugar, e faz suas colunas tremerem.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Ele dá ordem ao sol, e ele não brilha; e sela as estrelas.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Ele é o que sozinho estende os céus, e anda sobre as alturas do mar.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Ele é o que fez a Usra, o Órion, as Plêiades, e as constelações do sul.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Ele é o que faz coisas grandes e incompreensíveis, e inúmeras maravilhas.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Eis que ele passa diante de mim, sem que eu não o veja; ele passará diante de mim, sem que eu saiba.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Eis que, quando ele toma, quem pode lhe impedir? Quem poderá lhe dizer: O que estás fazendo?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Deus não reverterá sua ira, e debaixo dele se encurvam os assistentes de Raabe.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Como poderia eu lhe responder, e escolher minhas palavras contra ele?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
A ele, ainda que eu fosse justo, não lhe responderia; a meu juiz pediria misericórdia.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Ainda que eu lhe chamasse, e ele respondesse, mesmo assim não creria que ele tivesse dado ouvidos à minha voz.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Pois ele tem me quebrantado com tempestade, e multiplicado minhas feridas sem causa.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Ele não me permite respirar; em vez disso, me farta de amarguras.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Quanto às forças, eis que ele é forte; e quanto ao juízo, [ele diria]: Quem me convocará?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Ainda que eu seja justo, minha boca me condenaria; se eu fosse inocente, então ela me declararia perverso.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Mesmo se eu for inocente, não estimo minha alma; desprezo minha vida.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
É tudo a mesma coisa; por isso digo: ele consome ao inocente e ao perverso.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Quando o açoite mata de repente, ele ri do desespero dos inocentes.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
A terra está entregue nas mãos dos perversos. Ele cobre o rosto de seus juízes. Se não é ele, então quem é?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Meus dias foram mais rápidos que um homem que corre; fugiram, e não viram o bem.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Passaram como barcos de papiro, como a águia que se lança à comida.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Se disser: Esquecerei minha queixa, mudarei o aspecto do meu rosto, e sorrirei,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
[Ainda] teria pavor de todas as minhas dores; [pois] sei que não me terás por inocente.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Se eu já estou condenado, então para que eu sofreria em vão?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Ainda que me lave com água de neve, e limpe minhas mãos com sabão,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Então me submergirias no fosso, e minhas próprias vestes me abominariam.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Pois ele não é homem como eu, para que eu lhe responda, e venhamos juntamente a juízo.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Não há entre nós árbitro que ponha sua mão sobre nós ambos,
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Tire de sobre mim sua vara, e seu terror não me espante.
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
[Então] eu falaria, e não teria medo dele. Pois não está sendo assim comigo.

< Ayuba 9 >