< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
UJobe wasephendula wathi:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Ngeqiniso ngiyazi ukuthi kunjalo. Kodwa umuntu angalunga njani kuNkulunkulu?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Uba efisa ukuphikisana laye, kayikumphendula okukodwa phakathi kwenkulungwane.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Uhlakaniphile enhliziyweni, uqinile emandleni: Ngubani oziqinisileyo wamelana laye waphumelela?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Osusa izintaba njalo zingazi, ozigenqula entukuthelweni yakhe.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Onyikinya umhlaba awususe endaweni yawo, lensika zawo zizamazame.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Olaya ilanga ukuthi lingaphumi, avalele inkanyezi ngophawu.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Owendlala amazulu eyedwa, anyathele phezu kwezingqonga zolwandle.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Owenza iBhere, iziNja, lesiLimela, lamakamelo eningizimu.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Owenza izinto ezinkulu ezingelakuhlolwa, lezimangalisayo ezingelakubalwa.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Khangela, uyedlula phansi kwami ngingamboni, edlulele phambili ngingamuzwa.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Khangela, uyahluthuna, ngubani ongamnqanda? Ngubani ongathi kuye: Wenzani?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
UNkulunkulu kayinqandi intukuthelo yakhe. Abasizi bakaRahabi bayakhothama phansi kwakhe.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Pho-ke, mina ngingamphendula ngithini, ngikhethe amazwi ami okuqondana laye?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Ebengingeke ngamphendula loba bengilungile; ngizacela isihawu kumahluleli wami.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Uba bengibizile, wangiphendula, bengingayikukholwa ukuthi ubekile indlebe elizwini lami.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Ngoba uyangihlifiza ngesiphepho, andise amanxeba ami kungelasizatho.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Kangivumeli ukukhokha umoya, kodwa engigcwalisa ngezinto ezibabayo.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Uba kungamandla, khangela, ulamandla. Njalo uba kungesahlulelo, ngubani ozangibiza?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Aluba ngilungile, umlomo wami uzangilahla; uba ngiphelele, uzakuthi ngonakele.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Ngiphelele, angikhathaleli umphefumulo wami, ngidelela impilo yami.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Kunye lokho, ngenxa yalokho ngithi: Uyabhubhisa olungileyo lomubi.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Lapho isiswepu sibulala ngokujumayo, uzahleka ukudangala kwabangelacala.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
Umhlaba unikelwe esandleni somubi; wembesa ubuso babehluleli bawo. Uba kungenjalo, pho, ngubani?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Njalo insuku zami zilejubane kulesigijimi; ziyabaleka, kaziboni okuhle.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Ziyedlula njengezikepe zomhlanga, njengokhozi olutheleka empangweni.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Uba ngisithi: Ngizakhohlwa ukusola kwami, ngitshiye ukunyukumala kwami, ngithokoze,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
ngiyesaba zonke insizi zami, ngiyazi ukuthi kawuyikungiphatha njengongelacala.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Ngilecala mina, pho, ngizatshikatshikelelani ize?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Uba ngizigezisa ngamanzi eliqhwa elikhithikileyo, ngihlambulule izandla zami ngesepa,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
khona uzangiphosela emgodini, besengisenyanywa yizigqoko zami.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Ngoba kasuye umuntu njengami ukuze ngimphendule, ukuze siye ndawonye kusahlulelo.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Kakukho umqamuli phakathi kwethu ongabeka isandla sakhe phezu kwethu sobabili.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Kasuse uswazi lwakhe kimi, njalo uvalo ngaye lungangethusi.
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Bengingakhuluma ngingamesabi, kodwa anginjalo ngokwami.

< Ayuba 9 >