< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Allora Giobbe rispose e disse:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
“Sì, certo, io so ch’egli e così; e come sarebbe il mortale giusto davanti a Dio?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Se all’uomo piacesse di piatir con Dio, non potrebbe rispondergli sovra un punto fra mille.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Dio è savio di cuore, è grande in potenza; chi gli ha tenuto fronte e se n’è trovato bene?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Egli trasporta le montagne senza che se ne avvedano, nel suo furore le sconvolge.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Egli scuote la terra dalle sue basi, e le sue colonne tremano.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Comanda al sole, ed esso non si leva; mette un sigillo sulle stelle.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Da solo spiega i cieli, e cammina sulle più alte onde del mare.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
E’ il creatore dell’Orsa, d’Orione, delle Pleiadi, e delle misteriose regioni del cielo australe.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Egli fa cose grandi e imperscrutabili, maraviglie senza numero.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Ecco, ei mi passa vicino, ed io nol veggo; mi scivola daccanto e non me n’accorgo.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Ecco afferra la preda, e chi si opporrà? Chi oserà dirgli: “Che fai?”
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Iddio non ritira la sua collera; sotto di lui si curvano i campioni della superbia.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
E io, come farei a rispondergli, a sceglier le mie parole per discuter con lui?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Avessi anche ragione, non gli replicherei, ma chiederei mercé al mio giudice.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
S’io lo invocassi ed egli mi rispondesse, non però crederei che avesse dato ascolto alla mia voce;
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
egli che mi piomba addosso dal seno della tempesta, che moltiplica senza motivo le mie piaghe,
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
che non mi lascia riprender fiato, e mi sazia d’amarezza.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Se si tratta di forza, ecco, egli è potente; se di diritto, ei dice: “Chi mi fisserà un giorno per comparire”?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Fossi pur giusto, la mia bocca stessa mi condannerebbe; fossi pure integro, essa mi farebbe dichiarar perverso.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Integro! Sì, lo sono! di me non mi preme, io disprezzo la vita!
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Per me è tutt’uno! perciò dico: “Egli distrugge ugualmente l’integro ed il malvagio.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Se un flagello, a un tratto, semina la morte, egli ride dello sgomento degli innocenti.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
La terra è data in balìa dei malvagi; ei vela gli occhi ai giudici di essa; se non è lui, chi è dunque”?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
E i miei giorni se ne vanno più veloci d’un corriere; fuggono via senz’aver visto il bene;
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
passan rapidi come navicelle di giunchi, come l’aquila che piomba sulla preda.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Se dico: “Voglio dimenticare il mio lamento, deporre quest’aria triste e rasserenarmi”,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
sono spaventato di tutti i miei dolori, so che non mi terrai per innocente.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Io sarò condannato; perché dunque affaticarmi invano?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Quand’anche mi lavassi con la neve e mi nettassi le mani col sapone,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
tu mi tufferesti nel fango d’una fossa, le mie vesti stesse m’avrebbero in orrore.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Dio non è un uomo come me, perch’io gli risponda e che possiam comparire in giudizio assieme.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Non c’è fra noi un arbitro, che posi la mano su tutti e due!
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Ritiri Iddio d’addosso a me la sua verga; cessi dallo spaventarmi il suo terrore;
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
allora io parlerò senza temerlo, giacché sento di non essere quel colpevole che sembro.

< Ayuba 9 >