< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Felele pedig Jób, és monda:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Igaz, jól tudom, hogy így van; hogyan is lehetne igaz a halandó ember Istennél?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Ha perelni akarna ő vele, ezer közül egy sem felelhetne meg néki.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Bölcs szívű és hatalmas erejű: ki szegülhetne ellene, hogy épségben maradjon?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
A ki hegyeket mozdít tova, hogy észre se veszik, és megfordítja őket haragjában.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
A ki kirengeti helyéből a földet, úgy hogy oszlopai megrepedeznek.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
A ki szól a napnak és az fel nem kél, és bepecsételi a csillagokat.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
A ki egymaga feszítette ki az egeket, és a tenger hullámain tapos.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
A ki teremtette a gönczölszekeret, a kaszás csillagot és a fiastyúkot és a délnek titkos tárait.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
A ki nagy dolgokat cselekszik megfoghatatlanul, és csudákat megszámlálhatatlanul.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Ímé, elvonul mellettem, de nem látom, átmegy előttem, de nem veszem észre.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Ímé, ha elragad valamit, ki akadályozza meg; ki mondhatja néki: Mit cselekszel?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Ha az Isten el nem fordítja az ő haragját, alatta meghajolnak Ráháb czinkosai is.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Hogyan felelhetnék hát én meg ő néki, és lelhetnék vele szemben szavakat?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
A ki, ha szinte igazam volna, sem felelhetnék néki; kegyelemért könyörögnék ítélő birámhoz.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Ha segítségül hívnám és felelne is nékem, még sem hinném, hogy szavamat fülébe vevé;
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
A ki forgószélben rohan meg engem, és ok nélkül megsokasítja sebeimet.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Nem hagyna még lélekzetet se vennem, hanem keserűséggel lakatna jól.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Ha erőre kerülne a dolog? Ímé, ő igen erős; és ha ítéletre? Ki tűzne ki én nékem napot?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Ha igaznak mondanám magamat, a szájam kárhoztatna engem; ha ártatlannak: bűnössé tenne engemet.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Ártatlan vagyok, nem törődöm lelkemmel, útálom az életemet.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Mindegy ez! Azért azt mondom: elveszít ő ártatlant és gonoszt!
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Ha ostorával hirtelen megöl, neveti a bűntelenek megpróbáltatását.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
A föld a gonosz kezébe adatik, a ki az ő biráinak arczát elfedezi. Nem így van? Kicsoda hát ő?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Napjaim gyorsabbak valának a kengyelfutónál: elfutának, nem láttak semmi jót.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Ellebbentek, mint a gyorsan járó hajók, miként zsákmányára csap a keselyű.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Ha azt mondom: Nosza elfelejtem panaszomat, felhagyok haragoskodásommal és vidám leszek:
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Megborzadok az én mindenféle fájdalmamtól; tudom, hogy nem találsz bűntelennek engem.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Rossz ember vagyok én! Minek fáraszszam hát magamat hiába?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Ha hóvízzel mosakodom is meg, ha szappannal mosom is meg kezeimet:
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Akkor is a posványba mártanál engem és az én ruháim is útálnának engem.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Mert nem ember ő, mint én, hogy néki megfelelhetnék, és együtt pörbe állanánk.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Nincs is közöttünk igazlátó, a ki kezét közbe vethesse kettőnk között!
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Venné csak el rólam az ő veszszejét, és az ő rettentésével ne rettegtetne engem:
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Akkor szólanék és nem félnék tőle: mert nem így vagyok én magammal!

< Ayuba 9 >