< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
ויען איוב ויאמר׃
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
אמנם ידעתי כי כן ומה יצדק אנוש עם אל׃
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
אם יחפץ לריב עמו לא יעננו אחת מני אלף׃
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
חכם לבב ואמיץ כח מי הקשה אליו וישלם׃
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
המעתיק הרים ולא ידעו אשר הפכם באפו׃
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
המרגיז ארץ ממקומה ועמודיה יתפלצון׃
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
האמר לחרס ולא יזרח ובעד כוכבים יחתם׃
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
נטה שמים לבדו ודורך על במתי ים׃
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
עשה עש כסיל וכימה וחדרי תמן׃
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
עשה גדלות עד אין חקר ונפלאות עד אין מספר׃
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
הן יעבר עלי ולא אראה ויחלף ולא אבין לו׃
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
הן יחתף מי ישיבנו מי יאמר אליו מה תעשה׃
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
אלוה לא ישיב אפו תחתו שחחו עזרי רהב׃
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
אף כי אנכי אעננו אבחרה דברי עמו׃
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
אשר אם צדקתי לא אענה למשפטי אתחנן׃
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
אם קראתי ויענני לא אאמין כי יאזין קולי׃
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
אשר בשערה ישופני והרבה פצעי חנם׃
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
לא יתנני השב רוחי כי ישבעני ממררים׃
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
אם לכח אמיץ הנה ואם למשפט מי יועידני׃
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
אם אצדק פי ירשיעני תם אני ויעקשני׃
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
תם אני לא אדע נפשי אמאס חיי׃
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
אחת היא על כן אמרתי תם ורשע הוא מכלה׃
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
אם שוט ימית פתאם למסת נקים ילעג׃
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
ארץ נתנה ביד רשע פני שפטיה יכסה אם לא אפוא מי הוא׃
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
וימי קלו מני רץ ברחו לא ראו טובה׃
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
חלפו עם אניות אבה כנשר יטוש עלי אכל׃
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
אם אמרי אשכחה שיחי אעזבה פני ואבליגה׃
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
יגרתי כל עצבתי ידעתי כי לא תנקני׃
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
אנכי ארשע למה זה הבל איגע׃
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
אם התרחצתי במו שלג והזכותי בבר כפי׃
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
אז בשחת תטבלני ותעבוני שלמותי׃
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
כי לא איש כמני אעננו נבוא יחדו במשפט׃
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
לא יש בינינו מוכיח ישת ידו על שנינו׃
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
יסר מעלי שבטו ואמתו אל תבעתני׃
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
אדברה ולא איראנו כי לא כן אנכי עמדי׃

< Ayuba 9 >