< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Et, répondant, Job dit:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Assurément, je vois qu’il en est ainsi, et qu’un homme comparé à Dieu n’est pas trouvé juste.
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
S’il veut disputer avec lui, il ne pourra répondre une chose sur mille.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Dieu est sage de cœur et puissant en force: qui lui a résisté, et a eu la paix?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
C’est lui qui a transporté des montagnes, et ceux qu’il a renversés dans sa fureur ne s’en sont pas aperçus.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
C’est lui qui remue la terre de sa place, et fait que ses colonnes sont renversées.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
C’est lui qui commande au soleil, et le soleil ne se lève pas; et qui renferme les étoiles comme sous un sceau.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
C’est lui qui seul étend les cieux, et qui marche sur les flots de la mer.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
C’est lui qui a fait Arcturus, Orion, les Hyades et les astres cachés du midi.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
C’est lui qui fait des choses grandes, incompréhensibles et admirables qui sont sans nombre.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
S’il vient à moi, je ne le verrai pas: s’il s’en va, je ne m’en apercevrai pas.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
S’il interroge soudain, qui lui répondra? ou qui peut dire: Pourquoi faites-vous ainsi?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
C’est Dieu à la colère duquel personne ne peut résister, et sous qui se courbent ceux qui portent l’univers.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Combien grand suis-je donc moi, pour que je lui réponde et que je lui parle avec mes propres paroles?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Quand j’aurais en moi quel que justice, je ne répondrais rien, mais j’implorerais mon juge.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Lors même qu’il m’aurait exaucé, quand je l’invoquais, je ne croirais pas qu’il eût entendu ma voix.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Car il me brisera dans un tourbillon, et il multipliera mes plaies même sans raison.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Il ne permet pas que mon esprit se repose, et il me remplit d’amertumes.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Si j’ai recours à la force, il est très puissant; si à l’équité d’un jugement, personne n’ose rendre témoignage pour moi.
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Si je veux me justifier, ma propre bouche me condamnera; si je me montre innocent, il prouvera que je suis pervers.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Quand je serais juste, mon âme l’ignorerait même, et j’aurais du dégoût pour ma vie.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Je n’ai dit qu’une seule chose, c’est que Dieu détruit et l’innocent et l’impie.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
S’il frappe, qu’il tue tout d’un coup, et qu’il ne se rie pas des peines des innocents.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
La terre a été livrée aux mains de l’impie; il voile le visage de ses juges; que si ce n’est pas lui, qui est-ce donc?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Mes jours ont été plus rapides qu’un coureur: ils ont fui et n’ont pas vu de bonheur.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Ils ont passé comme des vaisseaux qui portent des fruits, comme un aigle qui vole vers sa pâture.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Lorsque je dis: Je ne parlerai plus ainsi, je change de visage, et je suis tourmenté par la douleur.
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Je redoutais toutes mes œuvres, sachant que vous ne me pardonneriez pas, si je péchais.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Et si après cela je suis impie, pourquoi ai-je travaillé en vain?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Si j’avais été lavé comme dans de l’eau de neige, et si mes mains brillaient comme étant très nettes,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Vous me plongeriez néanmoins dans la fange, et mes vêtements auraient horreur de moi.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Car je ne répondrai pas à un homme qui est semblable à moi, et qui peut être entendu en jugement avec moi et à l’égal de moi.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Il n’y a personne qui puisse nous reprendre l’un et l’autre, et mettre sa main entre les deux.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Qu’il retire de moi sa verge, et que sa terreur ne m’épouvante point.
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Je parlerai et ne le craindrai pas; car, effrayé, je ne puis répondre.

< Ayuba 9 >