< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Et Job prit la parole, et dit:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Certainement, je sais qu'il en est ainsi; et comment l'homme serait-il juste devant Dieu?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
S'il veut plaider avec lui, il ne lui répondra pas une fois sur mille.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Il est habile en son intelligence, et puissant en sa force: qui lui a résisté et s'en est bien trouvé?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Il transporte les montagnes, et elles ne le savent pas; il les bouleverse en sa fureur;
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Il fait trembler la terre sur sa base, et ses colonnes sont ébranlées.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Il parle au soleil, et le soleil ne se lève pas; et il met un sceau sur les étoiles.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Seul, il étend les cieux, et il marche sur les hauteurs de la mer.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Il a créé la grande Ourse, l'Orion, et la Pléiade, et les régions cachées du midi.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Il fait de grandes choses qu'on ne peut sonder, de merveilleuses choses qu'on ne peut compter.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Voici, il passe près de moi, et je ne le vois pas; il passe encore, et je ne l'aperçois pas.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
S'il ravit, qui le lui fera rendre? Qui lui dira: Que fais-tu?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Dieu ne revient pas sur sa colère; sous lui sont abattus les plus puissants rebelles.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Combien moins lui pourrais-je répondre, moi, et choisir mes paroles pour lui parler!
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Quand j'aurais raison, je ne lui répondrais pas; je demanderais grâce à mon juge!
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Si je le citais, et qu'il me répondît, je ne croirais pas qu'il voulût écouter ma voix,
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Lui qui fond sur moi dans une tempête, et qui multiplie mes plaies sans motif.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Il ne me permet point de reprendre haleine; il me rassasie d'amertume.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
S'il est question de force, il dit: “Me voilà! “S'il est question de droit: “Qui m'assigne? “
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Quand même je serais juste, ma bouche me condamnerait; je serais innocent, qu'elle me déclarerait coupable.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Je suis innocent. Je ne me soucie pas de vivre, je ne fais aucun cas de ma vie.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Tout se vaut! C'est pourquoi j'ai dit: Il détruit l'innocent comme l'impie.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Quand un fléau soudain répand la mort, il se rit des épreuves des innocents.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
La terre est livrée aux mains des méchants; il couvre les yeux de ceux qui la jugent. Si ce n'est lui, qui est-ce donc
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Mes jours ont été plus légers qu'un courrier; ils se sont enfuis, sans voir le bonheur;
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Ils ont glissé comme des barques de roseaux, comme l'aigle qui fond sur sa proie.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Si je dis: Je veux oublier ma plainte, quitter mon air triste, et reprendre ma sérénité,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Je suis effrayé de toutes mes douleurs: je sais que tu ne me jugeras pas innocent.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Moi, je suis condamné, pourquoi me fatiguer en vain?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Quand je me laverais dans la neige, quand je purifierais mes mains dans la potasse,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Tu me plongerais dans le fossé, et mes vêtements m'auraient en horreur.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Car il n'est pas un homme comme moi pour que je lui réponde, pour que nous allions ensemble en justice.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Il n'y a pas d'arbitre entre nous, qui pose sa main sur nous deux.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Qu'il ôte sa verge de dessus moi, et que ses terreurs ne me troublent plus!
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Alors je lui parlerai sans crainte; car, dans l'état où je me trouve, je ne suis plus à moi.

< Ayuba 9 >