< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Mais Job répondit, et dit:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Certainement je sais que cela est ainsi; et comment l'homme [mortel] se justifierait-il devant le [Dieu] Fort?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Si [Dieu] veut plaider avec lui, de mille articles il ne saurait lui répondre sur un seul.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
[Dieu] est sage de cœur, et puissant en force. Qui est-ce qui s'est opposé à lui, et s'en est bien trouvé?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Il transporte les montagnes, et quand il les renverse en sa fureur, elles n'en connaissent rien.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Il remue la terre de sa place, et ses piliers sont ébranlés.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Il parle au soleil, et le soleil ne se lève point; et c'est lui qui tient les étoiles sous son cachet.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
C'est lui seul qui étend les cieux; qui marche sur les hauteurs de la mer;
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Qui a fait le chariot, et l'Orion, et la Poussinière, et les signes qui sont au fond du Midi;
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Qui fait des choses si grandes qu'on ne les peut sonder; et tant de choses merveilleuses, qu'on ne les peut compter.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Voici, il passera près de moi, et je ne le verrai point; et il repassera, et je ne l'apercevrai point.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Voilà, s'il ravit, qui le lui fera rendre? et qui est-ce qui lui dira: Que fais-tu?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Dieu ne retire point sa colère, et les hommes superbes qui viennent au secours, sont abattus sous lui.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Combien moins lui répondrais-je, moi et arrangerais-je mes paroles contre lui?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Moi, je ne lui répondrai point, quand même je serais juste, [mais] je demanderai grâce à mon juge.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Si je l'invoque, et qu'il me réponde, [encore] ne croirai-je point qu'il ait écouté ma voix.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Car il m'a écrasé du milieu d'un tourbillon, et il a ajouté plaie sur plaie, sans que je l'aie mérité.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Il ne me permet point de reprendre haleine, mais il me remplit d'amertumes.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
S'il est question de savoir qui est le plus fort; voilà, il est fort; et [s'il est question d'aller] en justice, qui est-ce qui m'y fera comparaître?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Si je me justifie, ma propre bouche me condamnera; [si je me fais] parfait, il me convaincra d'être coupable.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Quand je serais parfait, je ne me soucierais pas de vivre, je dédaignerais la vie.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Tout revient à un; c'est pourquoi j'ai dit qu'il consume l'homme juste et le méchant.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
[Au moins] si le fléau [dont il frappe] faisait mourir tout aussitôt; [mais] il se rit de l'épreuve des innocents.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
[C'est par lui que] la terre est livrée entre les mains du méchant; c'est lui qui couvre la face des juges de la [terre]; et si ce n'est pas lui, qui est-ce donc?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Or mes jours ont été plus vite qu'un courrier; ils s'en sont fuis, et n'ont point vu de bien.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Ils ont passé [comme] des barques de poste; comme un aigle qui vole après la proie.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Si je dis: J'oublierai ma plainte, je renoncerai à ma colère, je me fortifierai;
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Je suis épouvanté de tous mes tourments. Je sais que tu ne me jugeras point innocent.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Je serai [trouvé] méchant; pourquoi travaillerais-je en vain?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Si je me lave dans de l'eau de neige, et que je nettoie mes mains dans la pureté,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Alors tu me plongeras dans un fossé, et mes vêtements m'auront en horreur.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Car il n'est pas comme moi un homme, pour que je lui réponde, [et] que nous allions ensemble en jugement.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
[Mais] il n'y a personne qui prît connaissance de la cause qui serait entre nous, [et] qui mît la main sur nous deux.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Qu'il ôte [donc] sa verge de dessus moi, et que la frayeur que j'ai de lui ne me trouble plus.
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Je parlerai, et je ne le craindrai point; mais dans l'état où je suis je ne suis point à moi-même.

< Ayuba 9 >