< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Et Job répondit et dit:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
En vérité, je sais qu’il en est ainsi. Mais comment l’homme sera-t-il juste devant Dieu?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
S’il se plaît à contester avec lui, il ne lui répondra pas sur un point entre mille.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Il est sage de cœur et puissant en force: qui s’est endurci contre lui et a prospéré?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Il transporte les montagnes, et elles ne savent pas qu’il les renverse dans sa colère;
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Il remue la terre de sa place, et ses colonnes tremblent;
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Il parle au soleil, et [le soleil] ne se lève pas; et sur les étoiles il met son sceau;
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Seul il étend les cieux et marche sur les hauteurs de la mer;
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Il fait la grande Ourse, Orion, et les Pléiades, et les chambres du midi;
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Il fait de grandes choses qu’on ne saurait sonder, et des merveilles à ne pouvoir les compter.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Voici, il passe près de moi, et je ne [le] vois pas; et il passe à côté [de moi], et je ne l’aperçois pas.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Voici, il ravit; qui l’en détournera? Qui lui dira: Que fais-tu?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Dieu ne retire pas sa colère; sous lui fléchissent les orgueilleux qui prêtent secours.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Combien moins lui répondrais-je, moi, [et] choisirais-je mes paroles avec lui!
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Si j’étais juste, je ne lui répondrais pas, je demanderais grâce à mon juge.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Si je criais, et qu’il me réponde, je ne croirais pas qu’il ait prêté l’oreille à ma voix, –
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Lui qui m’écrase dans une tempête, et qui multiplie mes blessures sans cause.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Il ne me permet pas de reprendre haleine; car il me rassasie d’amertumes.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
S’agit-il de force, voici, il est fort; s’agit-il de jugement: Qui m’assignera?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Si je me justifiais, ma bouche me condamnerait; si j’étais parfait, il me montrerait pervers.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Si j’étais parfait, je méconnaîtrais mon âme, je mépriserais ma vie.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Tout revient au même; c’est pourquoi j’ai dit: Il consume le parfait et le méchant.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Si le fléau donne subitement la mort, il se rit de l’épreuve de l’innocent.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
La terre est livrée en la main du méchant: il couvre la face de ses juges. S’il n’en est pas ainsi, qui est-ce donc?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Mes jours s’en vont plus vite qu’un coureur; ils fuient, ils ne voient pas ce qui est bon;
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Ils passent rapides comme les barques de jonc, comme un aigle qui fond sur sa proie.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Si je dis: J’oublierai ma plainte, je renoncerai à mon visage [morne] et je serai joyeux,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Je suis épouvanté de tous mes tourments; je sais que tu ne me tiendras pas pour innocent.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Soit, je suis méchant: pourquoi me fatigué-je ainsi en vain?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Si je me lave avec de l’eau de neige, et que je nettoie mes mains dans la pureté,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Alors tu me plongeras dans un fossé, et mes vêtements m’auront en horreur.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Car il n’est pas homme, comme moi, pour que je lui réponde, pour que nous allions ensemble en jugement.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Il n’y a pas entre nous un arbitre qui mettrait sa main sur nous deux.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Qu’il retire sa verge de dessus moi, et que sa terreur ne me trouble pas;
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Alors je parlerai et je ne le craindrai pas; mais il n’en est pas ainsi de moi.

< Ayuba 9 >