< Ayuba 9 >
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
“Yes, I certainly know that [much of] what you said is true. But (how can anyone say to God, ‘I (am innocent/have not done what is wrong) and prove it?’/no one can say to God ‘I (am innocent/have not done what is wrong) and prove it.’) [RHQ]
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
If someone wanted to argue with God [about that], God could ask him 1,000 questions, and that person would not be able to answer any of them!
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
God is very wise [IDM] and very powerful; no one who has tried to challenge God has been able to win.
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
He even moves mountains, without them (OR, anyone) knowing about it. When he is angry, he turns them upside down.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
He sends earthquakes that shake the ground; he causes the pillars that support the earth to tremble.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
[Some days] he speaks to the sun, and it does not rise, and [some nights] he prevents the stars from shining.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
He alone (stretched out/put in place) the sky; he alone puts his feet on the waves (OR, on the huge sea monster).
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
He put in their places [the clusters/groups of stars that are called] The Dipper/Bear, Orion, the Pleiades, and the stars in the southern sky.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Only he does great things that we cannot understand; he does more marvelous things than we are able to count.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
He passes by where I am, but I do not see him; he moves further on, but I do not see him go.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
If he [wants to] snatch something away, no one [RHQ] can hinder him; no one dares to ask him, ‘Why are you doing that?’ [RHQ]
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
God will not very easily stop being angry; he defeated [MTY] those who [tried to] help Rahab, [the great sea monster].
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
“So, [if God took me to court], what could I say [MTY] to answer him?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Even though I (would be innocent/would not have done what is wrong), I would not be able to answer him. All I could do would be to request God, my judge/accuser, to act mercifully toward me.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
If I summoned him to [come to the courtroom] and he said that he would come, I would not believe that he would pay attention to what I would say.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
He sends storms to batter me, and he bruises me many times (without any reason to do that/even though I am innocent).
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
[It is as though] he will not let me get/catch my breath, because he causes me to suffer all the time.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
If I would try to (wrestle with/fight against) him, [there is no way that I could defeat him, ] [because] he is stronger than I am. If I would request him to appear in court, there is no one who could [RHQ] force him to go there.
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Even though I was innocent, what I would say would cause him to say that I must be punished [MTY]; even though I had not done anything wrong, he would prove that I am guilty.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
“I have not done what is wrong, but that is not important. I despise continuing to remain alive.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
But it doesn’t matter, because God will get rid of [all of us, ] both those who are innocent and those who are wicked.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
When people experience disaster and it causes them to suddenly die, God laughs at it, even if they are innocent.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
God has allowed wicked people to control [what happens in] the world. [It is as though] he has caused judges to be blindfolded, [with the result that they cannot judge fairly]. If it is not God who has put wicked people in control, who has done it?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
“My days go by very quickly, like a fast runner; [it is as though] they run away, and nothing good happens to me on those days.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
My life goes by very rapidly, like a boat made from reeds sailing swiftly, or like an eagle that swoops down to seize a small animal.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
If I smile and say [to God], ‘I will forget what I am complaining about; I will stop looking sad and try to be cheerful/happy,’
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
then I become afraid because of all that I am suffering, because I know that God does not consider that I am innocent.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
He will (condemn me/declare that I should be punished), so why should I keep trying in vain [to defend myself]?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
If I washed myself with snow or cleansed my hands with lye/soap [to get rid of my guilt],
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
he would still throw me into a filthy pit; as a result [it would be as though] even my clothes would detest me.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
“God is not a human, as I am, so there is no way that I could answer him [to prove that I am innocent] if we went together to have a trial [in a courtroom].
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
There is no one to (mediate/hear us and decide who is right), no one who has authority over both of us [IDM].
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
I wish/desire that he would stop punishing [MTY] me, and that he would not continue to terrify me.
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
If he did that, I would declare [that I am innocent] without being afraid of him, because I know that I really have not [done what is wrong like God thinks that I have].”