< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Then responded Job, and said—
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Of a truth, I know that so it is, But how can a mortal be just with GOD?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
If he choose to contend with him, he cannot answer him, one of a thousand:
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Wise in heart, and alert in vigour, What man hath hardened himself against him, and prospered!
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Who removeth mountains, unawares, Who overturneth them in his anger;
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Who shaketh the earth, out of its place, and, the pillars thereof, shudder;
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Who commandeth the sun, and it breaketh not forth, and, about the stars, he putteth a seal;
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Who spreadeth out fire heavens, by himself alone! and marcheth along, on the heights of the sea;
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Who made the Bear, the Giant and the Cluster, and the chambers of the south;
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Who doeth great things, past finding out, and marvels, beyond number.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Lo! he cometh upon me, yet can I not see him, Yea he passeth on, yet can I not discern him.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Lo! he snatcheth away, who can bring it back? Who shall say unto him, What wouldst thou do?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
As for GOD, if he withdraw not his anger, under him, will have submitted themselves—the proud helpers.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
How much less that, I, should answer him, should choose my words with him?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Whom, though I were righteous, yet would I not answer, to be absolved, I would make supplication.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Though I had called, and he had answered me, I could not believe, that he would lend an ear to my voice.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
For, with a tempest, would he fall upon me, and would multiply my wounds without need;
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
He would not suffer me to recover my breath, for he would surfeit me with bitter things.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
If it regardeth vigour, bold is he! If justice, who could summon him?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
If I should justify myself, mine own mouth, would condemn me, —I blameless? then had it shewn me perverse.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
I blameless? I should not know my own soul, I should despise my own life!
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
One thing, there is, for which cause, I have said it, The blameless and the lawless, he bringeth to an end.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
If, a scourge, slay suddenly, at the despair of innocent ones, he mocketh.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
The earth, hath been given into the hand of a lawless one, The faces of her judges, he covereth, If not, then who is it?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
My days, therefore, are swifter than a runner, They have fled, they have seen no good.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
They have passed away with boats of paper-reed, like a vulture [which] rusheth upon food.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
If I say, I will forget my complaint, I will lay aside my sad countenance, and brighten up,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
I am afraid of all my pains, I know, that thou wilt not pronounce me innocent.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
I, shall be held guilty, —Wherefore then, in vain, should I toil?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Though I bathe myself in snow water, and cleanse, in cleanness itself, my hands,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Then, in a ditch, wouldst thou plunge me, and mine own clothes should abhor me:
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
For he is not a man like myself, whom I might answer, nor could we come together into judgment:
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
There is not, between us, a mediator, who might lay his hand upon us both.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Let him take from off me his rod, and, his terror, let it not startle me:
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
I could speak, and not be afraid of him, although, not so, am, I, in myself!

< Ayuba 9 >